A rãnar da kuke ganin ta dukan mai shãyar da mãma tanã shagala daga abin da ta
shãyar, kuma dukan mai ciki tanã haihuwar cikinta, kuma kanã ganin mutãne sunã
mãsu mãyẽ alhãli kuwa su bã mãsu mãye ba, amma azãbar Allah ce mai tsanani.
Ya ku mutãne! Idan kun kasance a cikin shakka a Tãshin ¡iyãma, to, lalle ne Mũ,
Man halittaku daga turɓaya, sa'an nan kuma daga gudãjin jini, sa'an nan kuma
daga taõka wadda ake halittãwa da wadda ba a halittawa dõmin, Mu bayyana muku.
Kuma Munã tab batar da abin da Muke so a cikin mahaifa zuwa ga wani ajali
ambatacce, sa'an nan kuma Munã fitar da ku kunã jãrĩri, sa'an nan kuma dõmin ku
kai ga cikar ƙarfinku. Kuma daga cikin ku akwai wanda ke mutuwa, kuma daga gare
ku akwai wanda ake mayarwa zuwa ga mafi ƙasƙancin rãyuwa dõmin kada ya san kõme
a bãyan ya sani. Kuma kanã ganin ƙasa shiru, sa'an nan idan Muka saukar da ruwa
a kanta, sai ta girgiza kuma ta kumbura, kuma ta tsirar da tsirrai daga kõwane
nau'i mai ban sha'awa.
Yanã mai karkatar da sãshensa dõmin ya ɓatar (da wasu) daga tafarkin Allah! Yanã
da wani wulãkanci a dũniya, kuma Munã ɗanɗana masa azãbar gõbara a Rãnar ¡iyãma.
Kuma daga mutãne akwai mai bauta wa Allah a kan wani gefe. Sa'an nan idan wani
alhẽri ya sãme shi, sai ya natsu da shi, kuma idan wata fitina ta sãme shi, sai
ya jũya bãya a kan fuskarsa. Yã yi hasãrar dũniya da Lãhira. Waccan ita ce
hasãra bayyananna.
Lalle ne Allah Yanã shigar da waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan
ƙwarai a cikin gidãjen Aljanna, ƙoramu na gudãna daga ƙarƙashinsu. Lalle ne
Allah Yanã aikata abin da Yake nufi.
Wanda ya kasance yanã zaton cẽwa Allah bã zai taimake shi ba a cikin dũniya da
Lãhira to sai ya mĩƙa wata igiya zuwa sama, sa'an nan kuma ya yanke ta, sa'an
nan ya dũba. Shin, ko lalle kaidinsa zai gusar da abin da yake ji na takaici?
Lalle ne waɗanda suka yi ĩmãni da waɗanda suka tũba (Yahũdu) da waɗanda suka
karkace (Saba'ãwa) da Nasãra da Majũsãwa da waɗanda suka yi shirka, lalle ne
Allah Yanã yin hukunci a tsakãninsu a Ranãr ¡iyãma.Lalle ne Allah Mahalarci ne a
kan dukkan kõme.
Ashe, ba ka gani ba, lalle Allah, wanda yake a cikin sammai da wanda yake a
cikin ƙasa yanã yin sujada a gare shi, da kuma rãna da watã da taurãri da
duwãtsu da itãce da dabbõbi, da kuma mãsu yawa daga mutãne? Kuma waɗansu mãsu
yawa azãba tã tabbata a kansu. Kuma wanda Allah Ya wulãkantar, to, bã ya da wani
mai girmamãwa. Kuma Lalle ne Allah Yanã aikata abin da Yake so.
waɗannan ƙungiyõyi biyu ne mãsu husũma, sun yi husũma ga sha'anin Ubangijinsu.
To, waɗanda suka kãfirta an yanka musu waɗansu tufafi daga wata irin wuta, anã
zuba tafasasshen ruwa daga bisa kãwunansu.
Lalle ne, Allah Yana shigar da waɗanda suka yi ĩmãni kuma suka aikata ayyukan
ƙwarai a cikin gidãjen Aljanna, ƙoramu sunã gudãna daga ƙarƙashinsu, anã ƙawãta
su, a cikinsu, da waɗansu mundãye na zĩnãri da lu'u-lu'u. Kuma tufãfinsu a
cikinsu alharĩni ne.
Lalle ne waɗanda suka kãfirta kuma suka taushe (mutãne) daga hanyar Allah da
masallaci mai alfarma wanda Muka sanya shi ga mutãne alhãli kuwa mazauni a ciki
da baƙauye daidai suke kuma wanda ya yi nufin karkatar da gaskiya a cikinsa da
zãlunci zã Mu ɗanɗana masa daga wata azãba mai raɗadi.
Kuma a lõkacin da Muka iyãkance wa Ibrãhim wurin ¦akin (Muka ce masa), "Kada ka
haɗa kõme da Ni ga bauta, kuma ka tsarkake ¦ãkiNa dõmin mãsu ɗawãfi da mãsu
tsayuwa da mãsu ruku'u da mãsu sujada.
"Kuma ka yi yẽkuwa ga mutãne da wajabcin Hajji su je maka suna mãsu tafiya da
ƙafãfu da kuma a kan kõwane maɗankwarin rãƙumi mãsu zuwa daga kõwane rango mai
zurfi."
"Dõmin su halarci abũbuwan amfãni a gare su, kuma su ambãci sunan Allah a cikin
'yan kwãnuka sanannu sabõda abin da Ya azurta su da shĩ daga dabbõbin jin dãɗi.
Sai ku ci daga gare su, kuma ku ciyar da matsattse matalauci."
Wancan ne. Kuma wanda ya girmama hukunce-hukuncen Allah to shĩ ne mafĩfĩci a
gare shi, a wurin Ubangijinsa. Kuma an halatta muku dabbõbin ni'ima fãce abin da
ake karantãwa a kanku. Sabõda haka ku nĩsanci ƙazanta daga gumãka kuma ku
nĩsanci ƙazanta daga shaidar zur.
Kuna mãsu tsayuwa ga gaskiya dõmin Allah, ba masu yin shirka da Shi ba. Kuma
wanda ya yi shirka da Allah, to, yanã kamar abin da ya fãɗo daga sama, sa'an nan
tsuntsãye su cafe shi, ko iska ta fãɗa da shi a cikin wani wuri mai nisa.
Kuna da waɗansu abũbuwan amfãni a cikinta (dabbar hadaya) har ya zuwa ga wani
ajali ambatacce, sa'an nan kuma wurin halattãta zuwa ga ¦ãkin 'yantacce ne.
Kuma ga kõwace al'umma Mun sanya ibãdar yanka, dõmin su ambaci sũnan Allah a kan
abin da Ya azurta su da shi daga dabbõbin ni'ima. Sa'an nan kuma Abin bautawarku
Abin bautawa ne Guda, sai ku sallama Masa. Kuma ka yi bushãra ga mãsu ƙanƙantar
da kai.
Waɗanda suke idan an ambaci Allah sai zukãtansu su firgita, da mãsu haƙuri a kan
abin da ya sãme su, da mãsu tsayar da salla, kuma sunã ciyarwa daga abin da Muka
azurta su.
Kuma rãƙuman, Mun sanya su a gare ku, a ibãdõjin Allah. Kunã da wani alhẽri
babba a cikinsu. Sai ku ambaci sũnan Allah a kansu sunã tsaye a kan ƙafãfu uku.
Sa'an nan idan sãsanninsu suka fãɗi, to, ku ci daga gare su, kuma ku ciyar da
mai wadar zũci da mai bara. Kamar haka Muka hõre muku su, tsammãninku kunã
gõdẽwa.
Nãmõminsu bã za su sãmi Allah ba haka jinainansu amma taƙawa daga gare ku tanã,
sãmun Sa. Kamar haka Ya hõre su sabõda ku dõmin ku girmama Allah sabõda shiriyar
da Ya yi muku. Kuma ka yi bushãra ga mãsu kyautata yi.
Waɗanda aka fitina daga gidajensu bã da wani hakki ba fãce sunã cẽwa,
Ubangijinmu Allah ne."Kuma ba dõmin tunkuɗẽwar Allah ga mutãne ba, sãshensu da
sãshe, haƙĩƙa, da an rũsa sauma'õ'in (Ruhbãnãwa) dã majãmi'õ'in Nasãra da
gidãjen ibãdar Yahudu da masallatai waɗanda ake ambatar Allah a cikinsu da yawa.
Kuma lalle, haƙĩƙa, Allah Yanã taimakon wanda yake taimakon Sa. Lalle Allah ne
haƙĩƙa Mai ƙarfi Mabuwãyi.
Waɗanda suke idan Muka bã su ĩko a cikin ƙasa sai su tsai da salla, kuma su
baybr da zakka kuma su yi umurni da abin da aka sani, kuma su hana daga abin da
ba a sani ba. Kuma ãƙibar al'amura ga Allah take.
Sa'an nan da yawa daga alƙarya, Muka halaka ta, alhãli kuwa tanã mai zalũnci sai
ta zama fãɗaɗɗa a kan rassanta, da yawa daga rĩjiya wadda aka wõfintar, da kuma
gidãjen sarauta maɗaukaka.
Shin, to, ba su yi tafiya ba a cikin ƙasa dõmin zukãta waɗanda zã su yi hankali
da su da kunnuwa da za su yi saurãre da su su kasance a gare su? Dõmin lalle ne
idãnun ba su makanta, amma zukãta waɗanda ke a cikin ƙirãza sũ ke makanta.
Kuma sunã nẽman ka yi gaggãwa da azãba, alhãli kuwa Allah bã zai sãɓa wa'adinSa
ba kuma lalle ne, yini ɗaya a wurin Ubangijinka kamar shẽkara dubu yake daga
abin da kuke ƙidãyãwa.
Kuma ba Mu aika wani manzo ba a gabãninka, kuma ba Mu umurci wani Annabi ba fãce
idan ya yi bũri, sai Shaiɗan ya jẽfa (wani abu) a cikin bũrinsa, sa'an nan Allah
Ya shãfe abin da Shaiɗan ke jefãwa. Sa'an nan kuma Allah Ya kyautata ãyõyinSa.
Kuma Allah Masani ne, Mai hikima.
Dõmin Ya sanya abin da Shaiɗan ke jẽfãwa ya zama fitina ga waɗanda a cikin
zukãtansu akwai cũta, da mãsu ƙẽƙasassun zukãtansu. Kuma lalle ne azzãlumai
haƙĩƙa, sunã a cikin sãɓãnimai nĩsa.
Kuma dõmin waɗanda aka bai wa ilmi su sani lalle shi ne gaskiya daga Ubangijinka
dõmin su yi ĩmãni da shi sabõda zukãtansu su natsu gare shi. Kuma lalle ne
Allah, haƙĩƙa, Mai shiryar da waɗanda suka yi ĩmãni ne zuwa ga hanya
madaidaiciya.
Kuma waɗanda suka kãfirta bã zã su gushe ba sunã a cikin shakka daga gare shi,
har Sa'a ta jẽ musu bisa ga abke, kõ kuwa azãbar wani yini bakarãre ta jẽ musu.
Mulki a rãnar nan ga Allah yake, Yanã hukunci a tsakãninsu. To, waɗanda suka yi
ĩmãni, kuma suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã a cikin gidãjen Aljannar ni'ima.
Kuma waɗanda suka yi hijira a cikin tafarkin Allah sa'an nan kuma aka kashe su,
kõ suka mutu, lalle ne Allah Yanã azurta su da arziki mai kyau. Kuma lalle ne
Allah, haƙĩƙa, Shĩ ne Mafi alhẽrin mãsu azurtãwa.
Wancan! Kuma wanda ya rãma azãba da misãlin abin da aka yi masa, sa'an nan kuma
aka zãlunce shi, lalle ne Allah Yanã taimakon sa. Lalle ne Allah haƙĩƙa Mai
yãfẽwa ne, Mai gãfara.
Wancan! sabõda lalle ne Allah, shĩ ne Gaskiya, kuma lalle ne, abin da suke kira
waninSa shi ne ƙarya. Kuma lalle ne Allah, Shĩ ne Maɗaukaki, Mai girma.
Shin ba ka gani ba, lalle ne Allah Ya hõre muku abin da yake a cikin ƙasa, kuma
jirãge sunã gudãna a cikin tẽku, da umurninSa kuma Yanã riƙe sama dõmin kada ta
fãɗi a kan ƙasa fãce da izninsa? Lalle ne Allah ga mutãne haƙĩƙa, Mai tausayi
ne, Mai jin ƙai.
Ga kõwace al'umma Mun sanya wurin yanka, su ne masu yin baiko gare Shi, sabõda
haka, kada su yi maka jãyayya a cikin al'amarin (hadaya). Kuma ka yi kira zuwa
ga Ubangijinka lalle kai kana a kan shiriya madaidaiciya.
Ashe, ba ka sani ba, lalle ne Allah Yanã sanin abin da yake a cikin sama da
ƙasa? Lalle ne wancan yanã cikin Littafi lalle wancan ga Allah mai sauƙi ne.
Kuma sunã bautãwa baicin Allah, abin da (Allah) bai saukar da wani dalili ba
game da shi, kuma abin da bã su da wani ilmi game da shi, kuma bãbu wani mai
taimako ga azzãlumai.
Kuma idan anã karanta ãyõyinMu bayyanannu a kansu kanã sanin abin ƙyãma a cikin
fuskõkin waɗanda suka kãfirta sunã kusa su yi danƙa ga waɗanda ke karãtun
ayõyinMu a kansu. Ka ce: "Shin to in gaya muku abin da yake mafi sharri daga
wannan? (Ita ce) Wuta." Allah Yã yi alkawarinta ga waɗanda suka kãfirta. Kuma
makõmarsu ta mũnana.
"Ya ku mutãne! An buga wani misãli, sai ku saurãra zuwa gare shi. Lalle ne
waɗanda kuke kira baicin Allah, bã zã su halitta ƙudã ba, kõ da sun tãru gare
shi, kuma idan ƙudãn ya ƙwãce musu wani abu, bã zã su kuɓutar da shi ba daga
gare shi. Mai nẽma da wanda ake nẽman gare shi sun raunana."
Kuma ku yi jihãdi a cikin (al'amarin) Allah, hakkin JihãdinSa. shĩ ne Ya zãɓe ku
alhãli kuwa bai sanya wani ƙunci ba a kanku a cikin addĩni. Bisa ƙudurcẽwar
ubanku Ibrãhĩm, shĩ ne ya yi muku sũna Musulmi daga gabãnin haka. Kuma a cikin
wannan (Littãfi ya yi muku sũna Musulmi), dõmin Manzo ya kasance mai shaida a
kanku, kũ kuma ku kasancemãsu shaida a kan mutãne. Sabõda haka ku tsayar da
salla kuma ku bãyar da zakka kuma ku amince da Allah, Shi ne Majiɓincinku.
Sãbõda haka mãdalla da Shi Ya zama Majiɓinci, mãdalla da Shi ya zama Mai
taimako.