Prev  

15. Surah Al-Hijr سورة الحجر

  Next  



1st Ayah  1  الأية ١الأولي
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
الر ۚ تِلْكَ آيَاتُ الْكِتَابِ وَقُرْآنٍ مُّبِينٍ
Alif-lam-ra tilka ayatualkitabi waqur-anin mubeen

Hausa
 
A. L̃. R. Waɗancan ãyoyin littãfi ne da abin karantãwa mai bayyanãwa.

Ayah  15:2  الأية
رُّبَمَا يَوَدُّ الَّذِينَ كَفَرُوا لَوْ كَانُوا مُسْلِمِينَ
Rubama yawaddu allatheenakafaroo law kanoo muslimeen

Hausa
 
Da yawa waɗanda suka kãfirta suke gũrin dã dai sun kasance Musulmi.

Ayah  15:3  الأية
ذَرْهُمْ يَأْكُلُوا وَيَتَمَتَّعُوا وَيُلْهِهِمُ الْأَمَلُ ۖ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ
Tharhum ya/kuloo wayatamattaAAoowayulhihimu al-amalu fasawfa yaAAlamoon

Hausa
 
Ka bar su su ci kuma su ji dãdi, kuma gũri ya shagaltar da su, sa'an nan da sannu zã su sani.

Ayah  15:4  الأية
وَمَا أَهْلَكْنَا مِن قَرْيَةٍ إِلَّا وَلَهَا كِتَابٌ مَّعْلُومٌ
Wama ahlakna min qaryatin illawalaha kitabun maAAloom

Hausa
 
Kuma ba Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da littafi sananne.

Ayah  15:5  الأية
مَّا تَسْبِقُ مِنْ أُمَّةٍ أَجَلَهَا وَمَا يَسْتَأْخِرُونَ
Ma tasbiqu min ommatin ajalahawama yasta/khiroon

Hausa
 
Wata al'umma bã ta gabãtar ajalinta, kuma bã zã su jinkirta ba.

Ayah  15:6  الأية
وَقَالُوا يَا أَيُّهَا الَّذِي نُزِّلَ عَلَيْهِ الذِّكْرُ إِنَّكَ لَمَجْنُونٌ
Waqaloo ya ayyuha allatheenuzzila AAalayhi aththikru innaka lamajnoon

Hausa
 
Suka ce: "Yã kai wanda aka saukar da Ambato (Alƙur'ãni) a kansa! Lalle ne kai, haƙĩƙa, mahaukaci ne."

Ayah  15:7  الأية
لَّوْ مَا تَأْتِينَا بِالْمَلَائِكَةِ إِن كُنتَ مِنَ الصَّادِقِينَ
Law ma ta/teena bilmala-ikatiin kunta mina assadiqeen

Hausa
 
"Dõmin me bã zã ka zo mana da malã'ĩku ba idan ka kasance daga mãsu gaskiya?"

Ayah  15:8  الأية
مَا نُنَزِّلُ الْمَلَائِكَةَ إِلَّا بِالْحَقِّ وَمَا كَانُوا إِذًا مُّنظَرِينَ
Ma nunazzilu almala-ikata illabilhaqqi wama kanoo ithan munthareen

Hausa
 
Bã Mu sassaukar da malã'iku fãce da gaskiya, bã zã su kasance, a wannan lõkacin, waɗanda ake yi wa jinkĩri ba.

Ayah  15:9  الأية
إِنَّا نَحْنُ نَزَّلْنَا الذِّكْرَ وَإِنَّا لَهُ لَحَافِظُونَ
Inna nahnu nazzalna aththikrawa-inna lahu lahafithoon

Hausa
 
Lalle Mũ ne, Muka saukar da Ambato (Alƙur'ãni), kuma lal1e Mũ, haƙĩƙa, Mãsu kiyayẽwane gare shi.

Ayah  15:10  الأية
وَلَقَدْ أَرْسَلْنَا مِن قَبْلِكَ فِي شِيَعِ الْأَوَّلِينَ
Walaqad arsalna min qablika feeshiyaAAi al-awwaleen

Hausa
 
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun aika Manzanni a cikin ƙungiyõyin farko, gabãninka.

Ayah  15:11  الأية
وَمَا يَأْتِيهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا كَانُوا بِهِ يَسْتَهْزِئُونَ
Wama ya/teehim min rasoolin illakanoo bihi yastahzi-oon

Hausa
 
Kuma wani Manzo bã ya zuwa gare su fãce sun kasance sunã mãsu, izgili a gare shi.

Ayah  15:12  الأية
كَذَٰلِكَ نَسْلُكُهُ فِي قُلُوبِ الْمُجْرِمِينَ
Kathalika naslukuhu fee quloobialmujrimeen

Hausa
 
Kamar wancan ne Muke shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.

Ayah  15:13  الأية
لَا يُؤْمِنُونَ بِهِ ۖ وَقَدْ خَلَتْ سُنَّةُ الْأَوَّلِينَ
La yu/minoona bihi waqad khalatsunnatu al-awwaleen

Hausa
 
Bã su yin ĩmãni da shi, kuma haƙĩƙa, hanyar mutãnen farko ta shige.

Ayah  15:14  الأية
وَلَوْ فَتَحْنَا عَلَيْهِم بَابًا مِّنَ السَّمَاءِ فَظَلُّوا فِيهِ يَعْرُجُونَ
Walaw fatahna AAalayhim babanmina assama-i fathalloo feehiyaAArujoon

Hausa
 
Kuma dã Mun bũɗe wata ƙõfa daga sama a kansu har suka wuni a ciki sunã tãkãwa.

Ayah  15:15  الأية
لَقَالُوا إِنَّمَا سُكِّرَتْ أَبْصَارُنَا بَلْ نَحْنُ قَوْمٌ مَّسْحُورُونَ
Laqaloo innama sukkirat absarunabal nahnu qawmun mashooroon

Hausa
 
Lalle ne dã sun ce: "Abin sani kawai, an rufe idãnuwanmu ne. Ã'a, mũ mutãne ne waɗanda aka sihirce."

Ayah  15:16  الأية
وَلَقَدْ جَعَلْنَا فِي السَّمَاءِ بُرُوجًا وَزَيَّنَّاهَا لِلنَّاظِرِينَ
Walaqad jaAAalna fee assama-iburoojan wazayyannaha linnathireen

Hausa
 
Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun sanya waɗansu masaukai a, cikin sama, kuma Muka ƙawãta ta ga masu kallo.

Ayah  15:17  الأية
وَحَفِظْنَاهَا مِن كُلِّ شَيْطَانٍ رَّجِيمٍ
Wahafithnahamin kulli shaytanin rajeem

Hausa
 
Kuma Muka kiyãye ta daga dukan Shaiɗani wanda ake jĩfa.

Ayah  15:18  الأية
إِلَّا مَنِ اسْتَرَقَ السَّمْعَ فَأَتْبَعَهُ شِهَابٌ مُّبِينٌ
Illa mani istaraqa assamAAafaatbaAAahu shihabun mubeen

Hausa
 
Fãce wanda ya sãci saurãre sai wutar yũlã bayyananniya ta bĩ shi.

Ayah  15:19  الأية
وَالْأَرْضَ مَدَدْنَاهَا وَأَلْقَيْنَا فِيهَا رَوَاسِيَ وَأَنبَتْنَا فِيهَا مِن كُلِّ شَيْءٍ مَّوْزُونٍ
Wal-arda madadnahawaalqayna feeha rawasiya waanbatnafeeha min kulli shay-in mawzoon

Hausa
 
Kuma ƙasa Mun mĩkẽ ta kuma Mun jẽfa duwãtsu tabbatattu a cikinta kuma Mun tsirar a cikinta, daga dukan abu wanda ake aunãwa da sikẽli.

Ayah  15:20  الأية
وَجَعَلْنَا لَكُمْ فِيهَا مَعَايِشَ وَمَن لَّسْتُمْ لَهُ بِرَازِقِينَ
WajaAAalna lakum feeha maAAayishawaman lastum lahu biraziqeen

Hausa
 
Kuma Muka sanyã muku, a cikinta, abũbuwan rãyuwã da wanda ba ku zamã mãsu ciyarwa gare shi ba.

Ayah  15:21  الأية
وَإِن مِّن شَيْءٍ إِلَّا عِندَنَا خَزَائِنُهُ وَمَا نُنَزِّلُهُ إِلَّا بِقَدَرٍ مَّعْلُومٍ
Wa-in min shay-in illa AAindanakhaza-inuhu wama nunazziluhu illa biqadarinmaAAloom

Hausa
 
Kuma bãbu wani abu fãce a wurinMu, akwai taskõkĩnsa kuma ba Mu saukar da shi ba fãce kan gwargwado sananne.

Ayah  15:22  الأية
وَأَرْسَلْنَا الرِّيَاحَ لَوَاقِحَ فَأَنزَلْنَا مِنَ السَّمَاءِ مَاءً فَأَسْقَيْنَاكُمُوهُ وَمَا أَنتُمْ لَهُ بِخَازِنِينَ
Waarsalna arriyaha lawaqihafaanzalna mina assama-i maanfaasqaynakumoohu wama antum lahu bikhazineen

Hausa
 
Kuma Muka aika iskõki mãsu barbarar jũna sa'an nan Muka saukar da ruwa daga sama, sa'an nan Muka shãyar da ku shi, kuma ba ku zama mãsu taskacẽwa a gare shi ba.

Ayah  15:23  الأية
وَإِنَّا لَنَحْنُ نُحْيِي وَنُمِيتُ وَنَحْنُ الْوَارِثُونَ
Wa-inna lanahnu nuhyeewanumeetu wanahnu alwarithoon

Hausa
 
Kuma lalle ne Mu Muke rãyarwa, kuma Muke kashẽwa kuma Mũ ne magada.

Ayah  15:24  الأية
وَلَقَدْ عَلِمْنَا الْمُسْتَقْدِمِينَ مِنكُمْ وَلَقَدْ عَلِمْنَا الْمُسْتَأْخِرِينَ
Walaqad AAalimna almustaqdimeenaminkum walaqad AAalimna almusta/khireen

Hausa
 
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun san mãsu gabãta daga cikinku, kuma Mun san mãsu jinkiri.

Ayah  15:25  الأية
وَإِنَّ رَبَّكَ هُوَ يَحْشُرُهُمْ ۚ إِنَّهُ حَكِيمٌ عَلِيمٌ
Wa-inna rabbaka huwa yahshuruhuminnahu hakeemun AAaleem

Hausa
 
Kuma lalle ne Ubangijinka Shĩ ne Yake tãra su, lalle Shĩ ne Mai hikima, Masani.

Ayah  15:26  الأية
وَلَقَدْ خَلَقْنَا الْإِنسَانَ مِن صَلْصَالٍ مِّنْ حَمَإٍ مَّسْنُونٍ
Walaqad khalaqna al-insana minsalsalin min hama-in masnoon

Hausa
 
Kuma lalle ne Mun halicci mutum daga ƙeƙasasshiyar lãka, daga baƙin yumɓu wanda ya canja.

Ayah  15:27  الأية
وَالْجَانَّ خَلَقْنَاهُ مِن قَبْلُ مِن نَّارِ السَّمُومِ
Waljanna khalaqnahumin qablu min nari assamoom

Hausa
 
Kuma Aljani Mun haliccẽ shi daga gabãni, daga wutar iskar zafi.

Ayah  15:28  الأية
وَإِذْ قَالَ رَبُّكَ لِلْمَلَائِكَةِ إِنِّي خَالِقٌ بَشَرًا مِّن صَلْصَالٍ مِّنْ حَمَإٍ مَّسْنُونٍ
Wa-ith qala rabbuka lilmala-ikatiinnee khaliqun basharan min salsalin min hama-inmasnoon

Hausa
 
Kuma a lõkacin da Ubangijinka ya ce wa malã'iku: "Lalle Nĩ mai halittar wani jiki ne daga ƙẽƙasasshen yumɓu wanda ya canja."

Ayah  15:29  الأية
فَإِذَا سَوَّيْتُهُ وَنَفَخْتُ فِيهِ مِن رُّوحِي فَقَعُوا لَهُ سَاجِدِينَ
Fa-itha sawwaytuhu wanafakhtu feehimin roohee faqaAAoo lahu sajideen

Hausa
 
"To idan Na daidaitã shi kuma Na hũra daga RũhĩNa a cikinsa, to, ku fãɗi a gare shi, kunã mãsu yin sujada."

Ayah  15:30  الأية
فَسَجَدَ الْمَلَائِكَةُ كُلُّهُمْ أَجْمَعُونَ
Fasajada almala-ikatu kulluhumajmaAAoon

Hausa
 
Sai malã'iku suka yi sujada dukkansu gaba ɗaya.

Ayah  15:31  الأية
إِلَّا إِبْلِيسَ أَبَىٰ أَن يَكُونَ مَعَ السَّاجِدِينَ
Illa ibleesa aba an yakoonamaAAa assajideen

Hausa
 
Fãce Iblĩs, ya ƙi kasancẽwa daga mãsu yin sujadar.

Ayah  15:32  الأية
قَالَ يَا إِبْلِيسُ مَا لَكَ أَلَّا تَكُونَ مَعَ السَّاجِدِينَ
Qala ya ibleesu ma lakaalla takoona maAAa assajideen

Hausa
 
Ya ce: "Yã Iblĩs mẽne ne a gare ka, ba ka kasance tãre da mãsu yin sujuda ba?"

Ayah  15:33  الأية
قَالَ لَمْ أَكُن لِّأَسْجُدَ لِبَشَرٍ خَلَقْتَهُ مِن صَلْصَالٍ مِّنْ حَمَإٍ مَّسْنُونٍ
Qala lam akun li-asjuda libasharinkhalaqtahu min salsalin min hama-in masnoon

Hausa
 
Ya ce: "Ban kasance inã yin sujada ba ga mutum wanda Ka halicce shi daga bũsasshen yumɓun lãka wadda ta canja."

Ayah  15:34  الأية
قَالَ فَاخْرُجْ مِنْهَا فَإِنَّكَ رَجِيمٌ
Qala fakhruj minhafa-innaka rajeem

Hausa
 
Ya ce: "To, ka fita daga gare ta, dõmin lalle kai abin jĩfa ne."

Ayah  15:35  الأية
وَإِنَّ عَلَيْكَ اللَّعْنَةَ إِلَىٰ يَوْمِ الدِّينِ
Wa-inna AAalayka allaAAnata ila yawmiaddeen

Hausa
 
"Kuma lalle ne akwai la'ana a kanka har ya zuwa rãnar sakamako."

Ayah  15:36  الأية
قَالَ رَبِّ فَأَنظِرْنِي إِلَىٰ يَوْمِ يُبْعَثُونَ
Qala rabbi faanthirneeila yawmi yubAAathoon

Hausa
 
Ya ce: "Yã Ubangjĩna! Sai Ka yi mini jinkiri zuwa rãnar da ake tãshin su."

Ayah  15:37  الأية
قَالَ فَإِنَّكَ مِنَ الْمُنظَرِينَ
Qala fa-innaka mina almunthareen

Hausa
 
Ya ce: "To, lalle ne kanã daga waɗanda ake yi wa jinkiri."

Ayah  15:38  الأية
إِلَىٰ يَوْمِ الْوَقْتِ الْمَعْلُومِ
Ila yawmi alwaqti almaAAloom

Hausa
 
"Zuwa ga Yinin Lõkacin nan sananne."

Ayah  15:39  الأية
قَالَ رَبِّ بِمَا أَغْوَيْتَنِي لَأُزَيِّنَنَّ لَهُمْ فِي الْأَرْضِ وَلَأُغْوِيَنَّهُمْ أَجْمَعِينَ
Qala rabbi bima aghwaytaneelaozayyinanna lahum fee al-ardi walaoghwiyannahumajmaAAeen

Hausa
 
Ya ce: "Yã Ubangijina! Inã rantsuwa da abin da Ka ɓatar da ni da shi, haƙĩƙa inã ƙawãta musu (rãyuwa) a cikin ƙasã kuma haƙĩƙa inã ɓatar da su gabã ɗaya."

Ayah  15:40  الأية
إِلَّا عِبَادَكَ مِنْهُمُ الْمُخْلَصِينَ
Illa AAibadaka minhumualmukhlaseen

Hausa
 
"Fãce bãyinKa daga gare su, waɗanda Ka tsarkake."

Ayah  15:41  الأية
قَالَ هَٰذَا صِرَاطٌ عَلَيَّ مُسْتَقِيمٌ
Qala hatha siratunAAalayya mustaqeem

Hausa
 
Ya ce: "Wannan tafarki ne a gare Ni, madaidaici."

Ayah  15:42  الأية
إِنَّ عِبَادِي لَيْسَ لَكَ عَلَيْهِمْ سُلْطَانٌ إِلَّا مَنِ اتَّبَعَكَ مِنَ الْغَاوِينَ
Inna AAibadee laysa laka AAalayhimsultanun illa mani ittabaAAaka mina alghaween

Hausa
 
"Lalle ne bãyĩNa, bã ka da ĩkõ a kansu, fãce wanda ya bĩ ka daga ɓatattu."

Ayah  15:43  الأية
وَإِنَّ جَهَنَّمَ لَمَوْعِدُهُمْ أَجْمَعِينَ
Wa-inna jahannama lamawAAiduhum ajmaAAeen

Hausa
 
Kuma lalle Jahannama ce haƙĩƙa, ma'a1kawartarsu gabã ɗaya.

Ayah  15:44  الأية
لَهَا سَبْعَةُ أَبْوَابٍ لِّكُلِّ بَابٍ مِّنْهُمْ جُزْءٌ مَّقْسُومٌ
Laha sabAAatu abwabin likullibabin minhum juz-on maqsoom

Hausa
 
Tanã da ƙõfõfi bakwai, ga kõwace ƙõfa akwai wani juz'i daga gare su rababbe.

Ayah  15:45  الأية
إِنَّ الْمُتَّقِينَ فِي جَنَّاتٍ وَعُيُونٍ
Inna almuttaqeena fee jannatinwaAAuyoon

Hausa
 
Lalle mãsu taƙawa sunã a cikin gidãjen Aljanna mai idandunan ruwa.

Ayah  15:46  الأية
ادْخُلُوهَا بِسَلَامٍ آمِنِينَ
Odkhulooha bisalamin amineen

Hausa
 
"Ku shigẽ ta da aminci, kunã amintattu."

Ayah  15:47  الأية
وَنَزَعْنَا مَا فِي صُدُورِهِم مِّنْ غِلٍّ إِخْوَانًا عَلَىٰ سُرُرٍ مُّتَقَابِلِينَ
WanazaAAna ma fee sudoorihimmin ghillin ikhwanan AAala sururin mutaqabileen

Hausa
 
Kuma Muka ɗẽbe abinda ke a cikin zukãtansu na daga ƙullin zũci, suka zama 'yan'uwa a kan gadãje, sunã mãsu fuskantar junã.

Ayah  15:48  الأية
لَا يَمَسُّهُمْ فِيهَا نَصَبٌ وَمَا هُم مِّنْهَا بِمُخْرَجِينَ
La yamassuhum feeha nasabunwama hum minha bimukhrajeen

Hausa
 
Wata wahala bã zã ta shãfe su bã a cikinta kuma ba su zama mãsu fita daga, cikinta ba.

Ayah  15:49  الأية
نَبِّئْ عِبَادِي أَنِّي أَنَا الْغَفُورُ الرَّحِيمُ
Nabbi/ AAibadee annee anaalghafooru arraheem

Hausa
 
Ka bai wa bãyiNa lãbari cẽwa lalle ne Ni, Mai gãfarane, Mai jin ƙai.

Ayah  15:50  الأية
وَأَنَّ عَذَابِي هُوَ الْعَذَابُ الْأَلِيمُ
Waanna AAathabee huwa alAAathabual-aleem

Hausa
 
Kuma azãbãTa ita ce azãba mai raɗaɗi.

Ayah  15:51  الأية
وَنَبِّئْهُمْ عَن ضَيْفِ إِبْرَاهِيمَ
Wanabbi/hum AAan dayfi ibraheem

Hausa
 
Kuma ka bã su lãbãrin bãƙin Ibrãhĩm.

Ayah  15:52  الأية
إِذْ دَخَلُوا عَلَيْهِ فَقَالُوا سَلَامًا قَالَ إِنَّا مِنكُمْ وَجِلُونَ
Ith dakhaloo AAalayhi faqaloosalaman qala inna minkum wajiloon

Hausa
 
A lõkacin da suka shiga gunsa, sai suka ce: "Sallama." Ya ce: "Lalle mũ, daga gare ku, mãsu firgita ne."

Ayah  15:53  الأية
قَالُوا لَا تَوْجَلْ إِنَّا نُبَشِّرُكَ بِغُلَامٍ عَلِيمٍ
Qaloo la tawjal innanubashshiruka bighulamin AAaleem

Hausa
 
Suka ce: "Kada ka firgita. Lalle ne mũ, munã yi makabushãra game da wani yãro masani."

Ayah  15:54  الأية
قَالَ أَبَشَّرْتُمُونِي عَلَىٰ أَن مَّسَّنِيَ الْكِبَرُ فَبِمَ تُبَشِّرُونَ
Qala abashshartumoonee AAalaan massaniya alkibaru fabima tubashshiroon

Hausa
 
Ya ce: "Shin kun bã ni bushãra ne a kan tsũfa yã shãfe ni? To, da me kuke bã ni bushara?"

Ayah  15:55  الأية
قَالُوا بَشَّرْنَاكَ بِالْحَقِّ فَلَا تَكُن مِّنَ الْقَانِطِينَ
Qaloo bashsharnaka bilhaqqifala takun mina alqaniteen

Hausa
 
Suka ce: "Munã yi maka bushãra da gaskiya ne, sabõda haka, kada da kasance daga mãsu yanke tsammãni."

Ayah  15:56  الأية
قَالَ وَمَن يَقْنَطُ مِن رَّحْمَةِ رَبِّهِ إِلَّا الضَّالُّونَ
Qala waman yaqnatu min rahmatirabbihi illa addalloon

Hausa
 
Ya ce: "Kuma wãne ne yake yanke tsammãni daga rahamar Ubangijinsa, fãce ɓatattu?"

Ayah  15:57  الأية
قَالَ فَمَا خَطْبُكُمْ أَيُّهَا الْمُرْسَلُونَ
Qala fama khatbukumayyuha almursaloon

Hausa
 
Ya ce: "To, mẽne ne babban al'amarinku? Yã kũ manzanni!"

Ayah  15:58  الأية
قَالُوا إِنَّا أُرْسِلْنَا إِلَىٰ قَوْمٍ مُّجْرِمِينَ
Qaloo inna orsilna ilaqawmin mujrimeen

Hausa
 
Suka ce: "Lalle ne mũ, an aika mu zuwa ga wasu mutãne mãsu laifi."

Ayah  15:59  الأية
إِلَّا آلَ لُوطٍ إِنَّا لَمُنَجُّوهُمْ أَجْمَعِينَ
Illa ala lootin innalamunajjoohum ajmaAAeen

Hausa
 
"Fãce mutãnen Lũɗu, lalle ne mũ,haƙĩƙa, mãsu tsĩrar dasu ne gabã ɗaya."

Ayah  15:60  الأية
إِلَّا امْرَأَتَهُ قَدَّرْنَا ۙ إِنَّهَا لَمِنَ الْغَابِرِينَ
Illa imraatahu qaddarna innahalamina alghabireen

Hausa
 
"Fãce mãtarsa mun ƙaddara cẽwa lalle ne ita, haƙĩƙa, tanã daga mãsu halaka."

Ayah  15:61  الأية
فَلَمَّا جَاءَ آلَ لُوطٍ الْمُرْسَلُونَ
Falamma jaa ala lootinalmursaloon

Hausa
 
To, a lõkacin da mazannin suka jẽ wa mutãnen Lũɗu,

Ayah  15:62  الأية
قَالَ إِنَّكُمْ قَوْمٌ مُّنكَرُونَ
Qala innakum qawmun munkaroon

Hausa
 
Ya ce: "Lalle ne ku mutãne ne waɗanda ba a sani ba."

Ayah  15:63  الأية
قَالُوا بَلْ جِئْنَاكَ بِمَا كَانُوا فِيهِ يَمْتَرُونَ
Qaloo bal ji/naka bimakanoo feehi yamtaroon

Hausa
 
Suka ce: "Ã'a, mun zo maka sabõda abin da suka kasance sunã shakka a cikinsa."

Ayah  15:64  الأية
وَأَتَيْنَاكَ بِالْحَقِّ وَإِنَّا لَصَادِقُونَ
Waataynaka bilhaqqiwa-inna lasadiqoon

Hausa
 
"Kuma mun zo maka da gaskiya. Kuma lalle ne mũ, haƙĩƙa, mãsu gaskiya ne."

Ayah  15:65  الأية
فَأَسْرِ بِأَهْلِكَ بِقِطْعٍ مِّنَ اللَّيْلِ وَاتَّبِعْ أَدْبَارَهُمْ وَلَا يَلْتَفِتْ مِنكُمْ أَحَدٌ وَامْضُوا حَيْثُ تُؤْمَرُونَ
Faasri bi-ahlika biqitAAin minaallayli wattabiAA adbarahum wala yaltafitminkum ahadun wamdoo haythutu/maroon

Hausa
 
"Sai ka yi tafiya da iyãlinka, a wani yanki na dare, kuma ka bi bãyansu, kuma kada wani daga cikinku ya yi waiwaye, kuma ku bi ta inda aka aumurce ku."

Ayah  15:66  الأية
وَقَضَيْنَا إِلَيْهِ ذَٰلِكَ الْأَمْرَ أَنَّ دَابِرَ هَٰؤُلَاءِ مَقْطُوعٌ مُّصْبِحِينَ
Waqadayna ilayhi thalikaal-amra anna dabira haola-i maqtooAAunmusbiheen

Hausa
 
Kuma Muka hukunta wancan al'amarin zuwa gare shi cẽwa lalle ne ƙarshen waɗancan abin yankẽwa ne a lõkacin da suke mãsu shiga asuba.

Ayah  15:67  الأية
وَجَاءَ أَهْلُ الْمَدِينَةِ يَسْتَبْشِرُونَ
Wajaa ahlu almadeenati yastabshiroon

Hausa
 
Kuma mutãnen alƙaryar suka je sunã mãsu bushãra.

Ayah  15:68  الأية
قَالَ إِنَّ هَٰؤُلَاءِ ضَيْفِي فَلَا تَفْضَحُونِ
Qala inna haola-i dayfeefala tafdahoon

Hausa
 
Ya ce: "Lalle ne waɗannan bãƙĩna ne, sabõda haka kada ku kunyata ni."

Ayah  15:69  الأية
وَاتَّقُوا اللهَ وَلَا تُخْزُونِ
Wattaqoo Allaha walatukhzoon

Hausa
 
"Kuma ku bi Allah da taƙawa, kuma kada ku sanya ni a baƙin ciki."

Ayah  15:70  الأية
قَالُوا أَوَلَمْ نَنْهَكَ عَنِ الْعَالَمِينَ
Qaloo awa lam nanhaka AAani alAAalameen

Hausa
 
Suka ce: "Ashe ba mu hana ka daga tãlikai ba?"

Ayah  15:71  الأية
قَالَ هَٰؤُلَاءِ بَنَاتِي إِن كُنتُمْ فَاعِلِينَ
Qala haola-i banateein kuntum faAAileen

Hausa
 
Ya ce: "Ga waɗannan, 'ya'yãna idan kun kasance mãsu aikatãwa ne."

Ayah  15:72  الأية
لَعَمْرُكَ إِنَّهُمْ لَفِي سَكْرَتِهِمْ يَعْمَهُونَ
LaAAamruka innahum lafee sakratihimyaAAmahoona

Hausa
 
Rantsuwa da rãyuwarka! Lalle ne sũ a cikin mãyensu sunã ta ɗĩmuwa.

Ayah  15:73  الأية
فَأَخَذَتْهُمُ الصَّيْحَةُ مُشْرِقِينَ
Faakhathat-humu assayhatumushriqeen

Hausa
 
Sa'an nan tsãwa ta kãma su, sunã mãsu shiga lõkacin hũdõwar rãnã.

Ayah  15:74  الأية
فَجَعَلْنَا عَالِيَهَا سَافِلَهَا وَأَمْطَرْنَا عَلَيْهِمْ حِجَارَةً مِّن سِجِّيلٍ
FajaAAalna AAaliyaha safilahawaamtarna AAalayhim hijaratan minsijjeel

Hausa
 
Sa'an nan Muka sanya samanta ya kõma ƙasanta, kuma Muka yi ruwan duwãtsu na lãkar wuta a kansu.

Ayah  15:75  الأية
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَاتٍ لِّلْمُتَوَسِّمِينَ
Inna fee thalika laayatinlilmutawassimeen

Hausa
 
Lalle ne a cikin wancan akwai ãyõyi ga mãsu tsõkaci da hankali.

Ayah  15:76  الأية
وَإِنَّهَا لَبِسَبِيلٍ مُّقِيمٍ
Wa-innaha labisabeelin muqeem

Hausa
 
Kuma lalle ne ita, haƙĩƙa sunã a gẽfen wata hanyã tabbatacciya.

Ayah  15:77  الأية
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً لِّلْمُؤْمِنِينَ
Inna fee thalika laayatanlilmu/mineen

Hausa
 
Lalle ne a cikin wancan akwai ãyã ga mãsu ĩmãni.

Ayah  15:78  الأية
وَإِن كَانَ أَصْحَابُ الْأَيْكَةِ لَظَالِمِينَ
Wa-in kana as-habual-aykati lathalimeen

Hausa
 
Kuma lalle ne ma'abũta Al'aika sun kasance, haƙĩƙa, mãsu zãlunci!

Ayah  15:79  الأية
فَانتَقَمْنَا مِنْهُمْ وَإِنَّهُمَا لَبِإِمَامٍ مُّبِينٍ
Fantaqamna minhum wa-innahumalabi-imamin mubeen

Hausa
 
Sai Muka yi azãbar rãmuwã a gare su, kuma lalle sũ biyun, haƙĩƙa, sunã a gẽfen wani tafarki mabayyani.

Ayah  15:80  الأية
وَلَقَدْ كَذَّبَ أَصْحَابُ الْحِجْرِ الْمُرْسَلِينَ
Walaqad kaththaba as-habualhijri almursaleen

Hausa
 
Kuma lalle ne haƙĩƙa ma'abũta Hijiri sun ƙaryata Manzanni.

Ayah  15:81  الأية
وَآتَيْنَاهُمْ آيَاتِنَا فَكَانُوا عَنْهَا مُعْرِضِينَ
Waataynahum ayatinafakanoo AAanha muAArideen

Hausa
 
Kuma Kuka kai musu ãyõyinMu, sai suka kasance mãsu bijirẽwa daga gare su.

Ayah  15:82  الأية
وَكَانُوا يَنْحِتُونَ مِنَ الْجِبَالِ بُيُوتًا آمِنِينَ
Wakanoo yanhitoona mina aljibalibuyootan amineen

Hausa
 
Kuma sun kasance sunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, alhãli sunã amintattu.

Ayah  15:83  الأية
فَأَخَذَتْهُمُ الصَّيْحَةُ مُصْبِحِينَ
Faakhathat-humu assayhatumusbiheen

Hausa
 
Sai tsãwa ta kãma su sunã mãsu shiga asuba.

Ayah  15:84  الأية
فَمَا أَغْنَىٰ عَنْهُم مَّا كَانُوا يَكْسِبُونَ
Fama aghna AAanhum ma kanooyaksiboon

Hausa
 
Sa'an nan abin da suka kasance sunã tsirfantãwa bai wadãtar ga barinsu ba.

Ayah  15:85  الأية
وَمَا خَلَقْنَا السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ وَمَا بَيْنَهُمَا إِلَّا بِالْحَقِّ ۗ وَإِنَّ السَّاعَةَ لَآتِيَةٌ ۖ فَاصْفَحِ الصَّفْحَ الْجَمِيلَ
Wama khalaqna assamawatiwal-arda wama baynahuma illabilhaqqi wa-inna assaAAata laatiyatunfasfahi assafhaaljameel

Hausa
 
Kuma ba Mu halicci sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu ba fãce da gaskiya. Kuma lalle ne Sã'a (Rãnar Alƙiyãma) haƙĩƙa mai zuwa ce. Sabõdahaka ka yi rangwame, rangwame mai kyau.

Ayah  15:86  الأية
إِنَّ رَبَّكَ هُوَ الْخَلَّاقُ الْعَلِيمُ
Inna rabbaka huwa alkhallaqualAAaleem

Hausa
 
Lalle ne Ubangijinka, shi ne Mai yawan halitta, Masani.

Ayah  15:87  الأية
وَلَقَدْ آتَيْنَاكَ سَبْعًا مِّنَ الْمَثَانِي وَالْقُرْآنَ الْعَظِيمَ
Walaqad ataynaka sabAAan minaalmathanee walqur-ana alAAatheem

Hausa
 
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun bã ka bakwai waɗanda ake maimaita karatunsu da Alƙur'ãni mai girma.

Ayah  15:88  الأية
لَا تَمُدَّنَّ عَيْنَيْكَ إِلَىٰ مَا مَتَّعْنَا بِهِ أَزْوَاجًا مِّنْهُمْ وَلَا تَحْزَنْ عَلَيْهِمْ وَاخْفِضْ جَنَاحَكَ لِلْمُؤْمِنِينَ
La tamuddanna AAaynayka ila mamattaAAna bihi azwajan minhum wala tahzanAAalayhim wakhfid janahaka lilmu/mineen

Hausa
 
Kada lalle kaƙĩƙa idãnunka biyu zuwa ga abin da Muka jiyar da su dãɗi game da shi, nau'i-nau'i a gare su, kuma kada ka yi baƙin ciki a kansu, kuma sassauta fikãfikanka ga mãsu ĩmãni.

Ayah  15:89  الأية
وَقُلْ إِنِّي أَنَا النَّذِيرُ الْمُبِينُ
Waqul innee ana annatheerualmubeen

Hausa
 
Kuma ka ce: "Lalle nĩ nĩ ne mai gargaɗi bayyananne."

Ayah  15:90  الأية
كَمَا أَنزَلْنَا عَلَى الْمُقْتَسِمِينَ
Kama anzalna AAalaalmuqtasimeen

Hausa
 
Kamar yadda Muka saukar a kan mãsu yin rantsuwa,

Ayah  15:91  الأية
الَّذِينَ جَعَلُوا الْقُرْآنَ عِضِينَ
Allatheena jaAAaloo alqur-anaAAideen

Hausa
 
Waɗanda suka sanya Alƙur'ãni tãtsuniyõyi.

Ayah  15:92  الأية
فَوَرَبِّكَ لَنَسْأَلَنَّهُمْ أَجْمَعِينَ
Fawarabbika lanas-alannahum ajmaAAeen

Hausa
 
To, rantsuwa da Ubangijinka! Haƙĩƙa, Munã tambayarsugabã ɗaya.

Ayah  15:93  الأية
عَمَّا كَانُوا يَعْمَلُونَ
AAamma kanoo yaAAmaloon

Hausa
 
Daga abin da suka kasance sunã aikatãwa.

Ayah  15:94  الأية
فَاصْدَعْ بِمَا تُؤْمَرُ وَأَعْرِضْ عَنِ الْمُشْرِكِينَ
FasdaAA bima tu/maruwaaAArid AAani almushrikeen

Hausa
 
Sai ka tsage gaskiya game da abin da ake umurnin ka kuma ka kau da kai daga masu shirki.

Ayah  15:95  الأية
إِنَّا كَفَيْنَاكَ الْمُسْتَهْزِئِينَ
Inna kafaynaka almustahzi-een

Hausa
 
Lalle ne Mũ Mun isar maka daga mãsu izgili.

Ayah  15:96  الأية
الَّذِينَ يَجْعَلُونَ مَعَ اللهِ إِلَٰهًا آخَرَ ۚ فَسَوْفَ يَعْلَمُونَ
Allatheena yajAAaloona maAAa Allahiilahan akhara fasawfa yaAAlamoon

Hausa
 
Waɗanda suke sanyãwar wani abin bautãwa na dabam tare da Allah, sa'an nan da sannu zã su sani.

Ayah  15:97  الأية
وَلَقَدْ نَعْلَمُ أَنَّكَ يَضِيقُ صَدْرُكَ بِمَا يَقُولُونَ
Walaqad naAAlamu annaka yadeequ sadrukabima yaqooloon

Hausa
 
Kuma lalle ne haƙĩƙa Munã sanin cẽwa lalle kai, ƙirjinka yanã yin ƙunci game da abin da suke faɗã (na izgili).

Ayah  15:98  الأية
فَسَبِّحْ بِحَمْدِ رَبِّكَ وَكُن مِّنَ السَّاجِدِينَ
Fasabbih bihamdi rabbika wakunmina assajideen

Hausa
 
Sabõda haka ka yi tasbĩhi game da gõde wa Ubangijinka, kuma ka kasance daga mãsu sujada.

Ayah  15:99  الأية
وَاعْبُدْ رَبَّكَ حَتَّىٰ يَأْتِيَكَ الْيَقِينُ
WaAAbud rabbaka hattaya/tiyaka alyaqeen

Hausa
 
Kuma ka bauta wa Ubangijinka, har mutuwa ta zo maka. 




© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us