Prev  

26. Surah Ash-Shu'arâ' سورة الشعراء

  Next  




1st Ayah  1  الأية ١الأولي
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
طسم
Ta-seen-meem

Hausa
 
¦. S̃. M̃.

Ayah  26:2  الأية
تِلْكَ آيَاتُ الْكِتَابِ الْمُبِينِ
Tilka ayatu alkitabialmubeen

Hausa
 
Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.

Ayah  26:3  الأية
لَعَلَّكَ بَاخِعٌ نَّفْسَكَ أَلَّا يَكُونُوا مُؤْمِنِينَ
LaAAallaka bakhiAAun nafsaka allayakoonoo mu/mineen

Hausa
 
Tsammãninka kai mai halakar da ranka ne, dõmin ba su kasance mũminai ba!

Ayah  26:4  الأية
إِن نَّشَأْ نُنَزِّلْ عَلَيْهِم مِّنَ السَّمَاءِ آيَةً فَظَلَّتْ أَعْنَاقُهُمْ لَهَا خَاضِعِينَ
In nasha/ nunazzil AAalayhim mina assama-iayatan fathallat aAAnaquhum lahakhadiAAeen

Hausa
 
Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.

Ayah  26:5  الأية
وَمَا يَأْتِيهِم مِّن ذِكْرٍ مِّنَ الرَّحْمَٰنِ مُحْدَثٍ إِلَّا كَانُوا عَنْهُ مُعْرِضِينَ
Wama ya/teehim min thikrin minaarrahmani muhdathin illa kanooAAanhu muAArideen

Hausa
 
Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa.

Ayah  26:6  الأية
فَقَدْ كَذَّبُوا فَسَيَأْتِيهِمْ أَنبَاءُ مَا كَانُوا بِهِ يَسْتَهْزِئُونَ
Faqad kaththaboo fasaya/teehim anbaoma kanoo bihi yastahzi-oon

Hausa
 
To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.

Ayah  26:7  الأية
أَوَلَمْ يَرَوْا إِلَى الْأَرْضِ كَمْ أَنبَتْنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوْجٍ كَرِيمٍ
Awa lam yaraw ila al-ardi kamanbatna feeha min kulli zawjin kareem

Hausa
 
Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau?

Ayah  26:8  الأية
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Inna fee thalika laayatan wamakana aktharuhum mu/mineen

Hausa
 
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.

Ayah  26:9  الأية
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Wa-inna rabbaka lahuwa alAAazeezu arraheem

Hausa
 
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.

Ayah  26:10  الأية
وَإِذْ نَادَىٰ رَبُّكَ مُوسَىٰ أَنِ ائْتِ الْقَوْمَ الظَّالِمِينَ
Wa-ith nada rabbukamoosa ani i/ti alqawma aththalimeen

Hausa
 
Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.

Ayah  26:11  الأية
قَوْمَ فِرْعَوْنَ ۚ أَلَا يَتَّقُونَ
Qawma firAAawna ala yattaqoon

Hausa
 
"Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?"

Ayah  26:12  الأية
قَالَ رَبِّ إِنِّي أَخَافُ أَن يُكَذِّبُونِ
Qala rabbi innee akhafu anyukaththiboon

Hausa
 
Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.

Ayah  26:13  الأية
وَيَضِيقُ صَدْرِي وَلَا يَنطَلِقُ لِسَانِي فَأَرْسِلْ إِلَىٰ هَارُونَ
Wayadeequ sadree walayantaliqu lisanee faarsil ila haroon

Hausa
 
"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.

Ayah  26:14  الأية
وَلَهُمْ عَلَيَّ ذَنبٌ فَأَخَافُ أَن يَقْتُلُونِ
Walahum AAalayya thanbun faakhafuan yaqtuloon

Hausa
 
"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."

Ayah  26:15  الأية
قَالَ كَلَّا ۖ فَاذْهَبَا بِآيَاتِنَا ۖ إِنَّا مَعَكُم مُّسْتَمِعُونَ
Qala kalla fathhababi-ayatina inna maAAakum mustamiAAoon

Hausa
 
Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."

Ayah  26:16  الأية
فَأْتِيَا فِرْعَوْنَ فَقُولَا إِنَّا رَسُولُ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Fa/tiya firAAawna faqoola innarasoolu rabbi alAAalameen

Hausa
 
"Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."

Ayah  26:17  الأية
أَنْ أَرْسِلْ مَعَنَا بَنِي إِسْرَائِيلَ
An arsil maAAana banee isra-eel

Hausa
 
"Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu."

Ayah  26:18  الأية
قَالَ أَلَمْ نُرَبِّكَ فِينَا وَلِيدًا وَلَبِثْتَ فِينَا مِنْ عُمُرِكَ سِنِينَ
Qala alam nurabbika feenawaleedan walabithta feena min AAumurika sineen

Hausa
 
Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"

Ayah  26:19  الأية
وَفَعَلْتَ فَعْلَتَكَ الَّتِي فَعَلْتَ وَأَنتَ مِنَ الْكَافِرِينَ
WafaAAalta faAAlataka allatee faAAaltawaanta mina alkafireen

Hausa
 
"Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?"

Ayah  26:20  الأية
قَالَ فَعَلْتُهَا إِذًا وَأَنَا مِنَ الضَّالِّينَ
Qala faAAaltuha ithanwaana mina addalleen

Hausa
 
Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin hushi."

Ayah  26:21  الأية
فَفَرَرْتُ مِنكُمْ لَمَّا خِفْتُكُمْ فَوَهَبَ لِي رَبِّي حُكْمًا وَجَعَلَنِي مِنَ الْمُرْسَلِينَ
Fafarartu minkum lamma khiftukumfawahaba lee rabbee hukman wajaAAalanee mina almursaleen

Hausa
 
"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."

Ayah  26:22  الأية
وَتِلْكَ نِعْمَةٌ تَمُنُّهَا عَلَيَّ أَنْ عَبَّدتَّ بَنِي إِسْرَائِيلَ
Watilka niAAmatun tamunnuha AAalayyaan AAabbadta banee isra-eel

Hausa
 
"Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla."

Ayah  26:23  الأية
قَالَ فِرْعَوْنُ وَمَا رَبُّ الْعَالَمِينَ
Qala firAAawnu wama rabbu alAAalameen

Hausa
 
Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"

Ayah  26:24  الأية
قَالَ رَبُّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا ۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ
Qala rabbu assamawatiwal-ardi wama baynahuma in kuntummooqineen

Hausa
 
Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."

Ayah  26:25  الأية
قَالَ لِمَنْ حَوْلَهُ أَلَا تَسْتَمِعُونَ
Qala liman hawlahu alatastamiAAoon

Hausa
 
Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"

Ayah  26:26  الأية
قَالَ رَبُّكُمْ وَرَبُّ آبَائِكُمُ الْأَوَّلِينَ
Qala rabbukum warabbu aba-ikumual-awwaleen

Hausa
 
Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."

Ayah  26:27  الأية
قَالَ إِنَّ رَسُولَكُمُ الَّذِي أُرْسِلَ إِلَيْكُمْ لَمَجْنُونٌ
Qala inna rasoolakumu allatheeorsila ilaykum lamajnoon

Hausa
 
Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."

Ayah  26:28  الأية
قَالَ رَبُّ الْمَشْرِقِ وَالْمَغْرِبِ وَمَا بَيْنَهُمَا ۖ إِن كُنتُمْ تَعْقِلُونَ
Qala rabbu almashriqi walmaghribiwama baynahuma in kuntum taAAqiloon

Hausa
 
Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."

Ayah  26:29  الأية
قَالَ لَئِنِ اتَّخَذْتَ إِلَٰهًا غَيْرِي لَأَجْعَلَنَّكَ مِنَ الْمَسْجُونِينَ
Qala la-ini ittakhathta ilahanghayree laajAAalannaka mina almasjooneen

Hausa
 
Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."

Ayah  26:30  الأية
قَالَ أَوَلَوْ جِئْتُكَ بِشَيْءٍ مُّبِينٍ
Qala awa law ji/tuka bishay-in mubeen

Hausa
 
Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"

Ayah  26:31  الأية
قَالَ فَأْتِ بِهِ إِن كُنتَ مِنَ الصَّادِقِينَ
Qala fa/ti bihi in kunta mina assadiqeen

Hausa
 
Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya."

Ayah  26:32  الأية
فَأَلْقَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ ثُعْبَانٌ مُّبِينٌ
Faalqa AAasahu fa-ithahiya thuAAbanun mubeen

Hausa
 
Sai ya jẽfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne.

Ayah  26:33  الأية
وَنَزَعَ يَدَهُ فَإِذَا هِيَ بَيْضَاءُ لِلنَّاظِرِينَ
WanazaAAa yadahu fa-itha hiya baydaolinnathireen

Hausa
 
Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo.

Ayah  26:34  الأية
قَالَ لِلْمَلَإِ حَوْلَهُ إِنَّ هَٰذَا لَسَاحِرٌ عَلِيمٌ
Qala lilmala-i hawlahu inna hathalasahirun AAaleem

Hausa
 
(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!

Ayah  26:35  الأية
يُرِيدُ أَن يُخْرِجَكُم مِّنْ أَرْضِكُم بِسِحْرِهِ فَمَاذَا تَأْمُرُونَ
Yureedu an yukhrijakum min ardikumbisihrihi famatha ta/muroon

Hausa
 
"Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mẽne ne kuke shãwartãwa?"

Ayah  26:36  الأية
قَالُوا أَرْجِهْ وَأَخَاهُ وَابْعَثْ فِي الْمَدَائِنِ حَاشِرِينَ
Qaloo arjih waakhahu wabAAathfee almada-ini hashireen

Hausa
 
Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."

Ayah  26:37  الأية
يَأْتُوكَ بِكُلِّ سَحَّارٍ عَلِيمٍ
Ya/tooka bikulli sahharin AAaleem

Hausa
 
"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."

Ayah  26:38  الأية
فَجُمِعَ السَّحَرَةُ لِمِيقَاتِ يَوْمٍ مَّعْلُومٍ
FajumiAAa assaharatu limeeqatiyawmin maAAloom

Hausa
 
Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne.

Ayah  26:39  الأية
وَقِيلَ لِلنَّاسِ هَلْ أَنتُم مُّجْتَمِعُونَ
Waqeela linnasi hal antummujtamiAAoon

Hausa
 
Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne?

Ayah  26:40  الأية
لَعَلَّنَا نَتَّبِعُ السَّحَرَةَ إِن كَانُوا هُمُ الْغَالِبِينَ
LaAAallana nattabiAAu assaharatain kanoo humu alghalibeen

Hausa
 
"Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya."

Ayah  26:41  الأية
فَلَمَّا جَاءَ السَّحَرَةُ قَالُوا لِفِرْعَوْنَ أَئِنَّ لَنَا لَأَجْرًا إِن كُنَّا نَحْنُ الْغَالِبِينَ
Falamma jaa assaharatuqaloo lifirAAawna a-inna lana laajran in kunnanahnu alghalibeen

Hausa
 
To, a lõkacin da masihirta suka jẽ suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?"

Ayah  26:42  الأية
قَالَ نَعَمْ وَإِنَّكُمْ إِذًا لَّمِنَ الْمُقَرَّبِينَ
Qala naAAam wa-innakum ithanlamina almuqarrabeen

Hausa
 
Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai."

Ayah  26:43  الأية
قَالَ لَهُم مُّوسَىٰ أَلْقُوا مَا أَنتُم مُّلْقُونَ
Qala lahum moosa alqoo maantum mulqoon

Hausa
 
Mũsã ya ce musu, "Ku jẽfa abin da kuke mãsu jẽfãwa."

Ayah  26:44  الأية
فَأَلْقَوْا حِبَالَهُمْ وَعِصِيَّهُمْ وَقَالُوا بِعِزَّةِ فِرْعَوْنَ إِنَّا لَنَحْنُ الْغَالِبُونَ
Faalqaw hibalahum waAAisiyyahumwaqaloo biAAizzati firAAawna inna lanahnualghaliboon

Hausa
 
Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."

Ayah  26:45  الأية
فَأَلْقَىٰ مُوسَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ تَلْقَفُ مَا يَأْفِكُونَ
Faalqa moosa AAasahufa-itha hiya talqafu ma ya/fikoon

Hausa
 
Sai Mũsa ya jẽfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya.

Ayah  26:46  الأية
فَأُلْقِيَ السَّحَرَةُ سَاجِدِينَ
Faolqiya assaharatu sajideen

Hausa
 
Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.

Ayah  26:47  الأية
قَالُوا آمَنَّا بِرَبِّ الْعَالَمِينَ
Qaloo amanna birabbialAAalameen

Hausa
 
Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."

Ayah  26:48  الأية
رَبِّ مُوسَىٰ وَهَارُونَ
Rabbi moosa waharoon

Hausa
 
"Ubangijin Mũsa da Hãrũna."

Ayah  26:49  الأية
قَالَ آمَنتُمْ لَهُ قَبْلَ أَنْ آذَنَ لَكُمْ ۖ إِنَّهُ لَكَبِيرُكُمُ الَّذِي عَلَّمَكُمُ السِّحْرَ فَلَسَوْفَ تَعْلَمُونَ ۚ لَأُقَطِّعَنَّ أَيْدِيَكُمْ وَأَرْجُلَكُم مِّنْ خِلَافٍ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمْ أَجْمَعِينَ
Qala amantum lahu qabla an athanalakum innahu lakabeerukumu allathee AAallamakumu assihrafalasawfa taAAlamoona laoqattiAAanna aydiyakum waarjulakummin khilafin walaosallibannakum ajmaAAeen

Hausa
 
Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa,zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya."

Ayah  26:50  الأية
قَالُوا لَا ضَيْرَ ۖ إِنَّا إِلَىٰ رَبِّنَا مُنقَلِبُونَ
Qaloo la dayra innaila rabbina munqaliboon

Hausa
 
Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."

Ayah  26:51  الأية
إِنَّا نَطْمَعُ أَن يَغْفِرَ لَنَا رَبُّنَا خَطَايَانَا أَن كُنَّا أَوَّلَ الْمُؤْمِنِينَ
Inna natmaAAu an yaghfira lanarabbuna khatayana an kunnaawwala almu/mineen

Hausa
 
"Lalle ne mu munã kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gãfarta mana kurakuranmu dõmin mun kasance farkon mãsu ĩmãni."

Ayah  26:52  الأية
وَأَوْحَيْنَا إِلَىٰ مُوسَىٰ أَنْ أَسْرِ بِعِبَادِي إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ
Waawhayna ila moosaan asri biAAibadee innakum muttabaAAoon

Hausa
 
Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cẽwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã ne.

Ayah  26:53  الأية
فَأَرْسَلَ فِرْعَوْنُ فِي الْمَدَائِنِ حَاشِرِينَ
Faarsala firAAawnu fee almada-ini hashireen

Hausa
 
Sai Fir'auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne.

Ayah  26:54  الأية
إِنَّ هَٰؤُلَاءِ لَشِرْذِمَةٌ قَلِيلُونَ
Inna haola-i lashirthimatunqaleeloon

Hausa
 
"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."

Ayah  26:55  الأية
وَإِنَّهُمْ لَنَا لَغَائِظُونَ
Wa-innahum lana lagha-ithoon

Hausa
 
"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."

Ayah  26:56  الأية
وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَاذِرُونَ
Wa-inna lajameeAAun hathiroon

Hausa
 
"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."

Ayah  26:57  الأية
فَأَخْرَجْنَاهُم مِّن جَنَّاتٍ وَعُيُونٍ
Faakhrajnahum min jannatinwaAAuyoon

Hausa
 
Sai Muka fitar da su daga gonaki da marẽmari.

Ayah  26:58  الأية
وَكُنُوزٍ وَمَقَامٍ كَرِيمٍ
Wakunoozin wamaqamin kareem

Hausa
 
Da taskõki da mazauni mai kyau.

Ayah  26:59  الأية
كَذَٰلِكَ وَأَوْرَثْنَاهَا بَنِي إِسْرَائِيلَ
Kathalika waawrathnahabanee isra-eel

Hausa
 
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla.

Ayah  26:60  الأية
فَأَتْبَعُوهُم مُّشْرِقِينَ
FaatbaAAoohum mushriqeen

Hausa
 
Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.

Ayah  26:61  الأية
فَلَمَّا تَرَاءَى الْجَمْعَانِ قَالَ أَصْحَابُ مُوسَىٰ إِنَّا لَمُدْرَكُونَ
Falamma taraa aljamAAaniqala as-habu moosa innalamudrakoon

Hausa
 
Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."

Ayah  26:62  الأية
قَالَ كَلَّا ۖ إِنَّ مَعِيَ رَبِّي سَيَهْدِينِ
Qala kalla inna maAAiya rabbeesayahdeen

Hausa
 
Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."

Ayah  26:63  الأية
فَأَوْحَيْنَا إِلَىٰ مُوسَىٰ أَنِ اضْرِب بِّعَصَاكَ الْبَحْرَ ۖ فَانفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرْقٍ كَالطَّوْدِ الْعَظِيمِ
Faawhayna ila moosaani idrib biAAasaka albahra fanfalaqafakana kullu firqin kattawdi alAAatheem

Hausa
 
Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge, kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.

Ayah  26:64  الأية
وَأَزْلَفْنَا ثَمَّ الْآخَرِينَ
Waazlafna thamma al-akhareen

Hausa
 
Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can.

Ayah  26:65  الأية
وَأَنجَيْنَا مُوسَىٰ وَمَن مَّعَهُ أَجْمَعِينَ
Waanjayna moosa waman maAAahuajmaAAeen

Hausa
 
Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.

Ayah  26:66  الأية
ثُمَّ أَغْرَقْنَا الْآخَرِينَ
Thumma aghraqna al-akhareen

Hausa
 
Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.

Ayah  26:67  الأية
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Inna fee thalika laayatan wamakana aktharuhum mu/mineen

Hausa
 
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

Ayah  26:68  الأية
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Wa-inna rabbaka lahuwa alAAazeezu arraheem

Hausa
 
Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.

Ayah  26:69  الأية
وَاتْلُ عَلَيْهِمْ نَبَأَ إِبْرَاهِيمَ
Watlu AAalayhim nabaa ibraheem

Hausa
 
Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm.

Ayah  26:70  الأية
إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِ مَا تَعْبُدُونَ
Ith qala li-abeehi waqawmihi mataAAbudoon

Hausa
 
A sã'ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bauta wa?"

Ayah  26:71  الأية
قَالُوا نَعْبُدُ أَصْنَامًا فَنَظَلُّ لَهَا عَاكِفِينَ
Qaloo naAAbudu asnamanfanathallu laha AAakifeen

Hausa
 
Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."

Ayah  26:72  الأية
قَالَ هَلْ يَسْمَعُونَكُمْ إِذْ تَدْعُونَ
Qala hal yasmaAAoonakum ithtadAAoon

Hausa
 
Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?"

Ayah  26:73  الأية
أَوْ يَنفَعُونَكُمْ أَوْ يَضُرُّونَ
Aw yanfaAAoonakum aw yadurroon

Hausa
 
"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"

Ayah  26:74  الأية
قَالُوا بَلْ وَجَدْنَا آبَاءَنَا كَذَٰلِكَ يَفْعَلُونَ
Qaloo bal wajadna abaanakathalika yafAAaloon

Hausa
 
Suka ce: "Ã'a mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa."

Ayah  26:75  الأية
قَالَ أَفَرَأَيْتُم مَّا كُنتُمْ تَعْبُدُونَ
Qala afaraaytum ma kuntumtaAAbudoon

Hausa
 
Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"

Ayah  26:76  الأية
أَنتُمْ وَآبَاؤُكُمُ الْأَقْدَمُونَ
Antum waabaokumu al-aqdamoon

Hausa
 
"Kũ da ubanninku mafi daɗẽwa?"

Ayah  26:77  الأية
فَإِنَّهُمْ عَدُوٌّ لِّي إِلَّا رَبَّ الْعَالَمِينَ
Fa-innahum AAaduwwun lee illa rabbaalAAalameen

Hausa
 
"To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu."

Ayah  26:78  الأية
الَّذِي خَلَقَنِي فَهُوَ يَهْدِينِ
Allathee khalaqanee fahuwa yahdeen

Hausa
 
"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."

Ayah  26:79  الأية
وَالَّذِي هُوَ يُطْعِمُنِي وَيَسْقِينِ
Wallathee huwa yutAAimuneewayasqeen

Hausa
 
"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."

Ayah  26:80  الأية
وَإِذَا مَرِضْتُ فَهُوَ يَشْفِينِ
Wa-itha maridtu fahuwayashfeen

Hausa
 
"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."

Ayah  26:81  الأية
وَالَّذِي يُمِيتُنِي ثُمَّ يُحْيِينِ
Wallathee yumeetunee thummayuhyeen

Hausa
 
"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."

Ayah  26:82  الأية
وَالَّذِي أَطْمَعُ أَن يَغْفِرَ لِي خَطِيئَتِي يَوْمَ الدِّينِ
Wallathee atmaAAu anyaghfira lee khatee-atee yawma addeen

Hausa
 
"Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako."

Ayah  26:83  الأية
رَبِّ هَبْ لِي حُكْمًا وَأَلْحِقْنِي بِالصَّالِحِينَ
Rabbi hab lee hukman waalhiqneebissaliheen

Hausa
 
"Ya Ubangijĩna! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai."

Ayah  26:84  الأية
وَاجْعَل لِّي لِسَانَ صِدْقٍ فِي الْآخِرِينَ
WajAAal lee lisana sidqinfee al-akhireen

Hausa
 
"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya a cikin mutãnen ƙarshe."

Ayah  26:85  الأية
وَاجْعَلْنِي مِن وَرَثَةِ جَنَّةِ النَّعِيمِ
WajAAalnee min warathati jannati annaAAeem

Hausa
 
"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima."

Ayah  26:86  الأية
وَاغْفِرْ لِأَبِي إِنَّهُ كَانَ مِنَ الضَّالِّينَ
Waghfir li-abee innahu kanamina addalleen

Hausa
 
"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."

Ayah  26:87  الأية
وَلَا تُخْزِنِي يَوْمَ يُبْعَثُونَ
Wala tukhzinee yawma yubAAathoon

Hausa
 
"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."

Ayah  26:88  الأية
يَوْمَ لَا يَنفَعُ مَالٌ وَلَا بَنُونَ
Yawma la yanfaAAu malun walabanoon

Hausa
 
"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."

Ayah  26:89  الأية
إِلَّا مَنْ أَتَى اللهَ بِقَلْبٍ سَلِيمٍ
Illa man ata Allahabiqalbin saleem

Hausa
 
"Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki."

Ayah  26:90  الأية
وَأُزْلِفَتِ الْجَنَّةُ لِلْمُتَّقِينَ
Waozlifati aljannatu lilmuttaqeen

Hausa
 
Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.

Ayah  26:91  الأية
وَبُرِّزَتِ الْجَحِيمُ لِلْغَاوِينَ
Waburrizati aljaheemu lilghaween

Hausa
 
Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.

Ayah  26:92  الأية
وَقِيلَ لَهُمْ أَيْنَ مَا كُنتُمْ تَعْبُدُونَ
Waqeela lahum ayna ma kuntumtaAAbudoon

Hausa
 
Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"

Ayah  26:93  الأية
مِن دُونِ اللهِ هَلْ يَنصُرُونَكُمْ أَوْ يَنتَصِرُونَ
Min dooni Allahi hal yansuroonakumaw yantasiroon

Hausa
 
"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"

Ayah  26:94  الأية
فَكُبْكِبُوا فِيهَا هُمْ وَالْغَاوُونَ
Fakubkiboo feeha hum walghawoon

Hausa
 
Sai aka kikkife su a cikinta, su da halakakkun.

Ayah  26:95  الأية
وَجُنُودُ إِبْلِيسَ أَجْمَعُونَ
Wajunoodu ibleesa ajmaAAoon

Hausa
 
Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya.

Ayah  26:96  الأية
قَالُوا وَهُمْ فِيهَا يَخْتَصِمُونَ
Qaloo wahum feeha yakhtasimoon

Hausa
 
Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,

Ayah  26:97  الأية
تَاللهِ إِن كُنَّا لَفِي ضَلَالٍ مُّبِينٍ
Tallahi in kunna lafeedalalin mubeen

Hausa
 
"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."

Ayah  26:98  الأية
إِذْ نُسَوِّيكُم بِرَبِّ الْعَالَمِينَ
Ith nusawweekum birabbi alAAalameen

Hausa
 
"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.

Ayah  26:99  الأية
وَمَا أَضَلَّنَا إِلَّا الْمُجْرِمُونَ
Wama adallana illaalmujrimoon

Hausa
 
"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."

Ayah  26:100  الأية
فَمَا لَنَا مِن شَافِعِينَ
Fama lana min shafiAAeen

Hausa
 
"Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta."

Ayah  26:101  الأية
وَلَا صَدِيقٍ حَمِيمٍ
Wala sadeeqin hameem

Hausa
 
"Kuma bã mu da abõki, masõyi."

Ayah  26:102  الأية
فَلَوْ أَنَّ لَنَا كَرَّةً فَنَكُونَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ
Falaw anna lana karratan fanakoonamina almu/mineen

Hausa
 
"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"

Ayah  26:103  الأية
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Inna fee thalika laayatan wamakana aktharuhum mu/mineen

Hausa
 
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.

Ayah  26:104  الأية
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Wa-inna rabbaka lahuwa alAAazeezu arraheem

Hausa
 
Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Ayah  26:105  الأية
كَذَّبَتْ قَوْمُ نُوحٍ الْمُرْسَلِينَ
Kaththabat qawmu noohinalmursaleen

Hausa
 
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.

Ayah  26:106  الأية
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ نُوحٌ أَلَا تَتَّقُونَ
Ith qala lahum akhoohum noohunala tattaqoon

Hausa
 
A lõkacin da ɗan'uwansu, Nũhu, ya ce musu, "Shin, bã zã ku yi taƙawa ba?"

Ayah  26:107  الأية
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ
Innee lakum rasoolun ameen

Hausa
 
"Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce."

Ayah  26:108  الأية
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Fattaqoo Allaha waateeAAoon

Hausa
 
"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Ayah  26:109  الأية
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Wama as-alukum AAalayhi min ajrin inajriya illa AAala rabbi alAAalameen

Hausa
 
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

Ayah  26:110  الأية
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Fattaqoo Allaha waateeAAoon

Hausa
 
"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Ayah  26:111  الأية
قَالُوا أَنُؤْمِنُ لَكَ وَاتَّبَعَكَ الْأَرْذَلُونَ
Qaloo anu/minu laka wattabaAAakaal-arthaloon

Hausa
 
Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"

Ayah  26:112  الأية
قَالَ وَمَا عِلْمِي بِمَا كَانُوا يَعْمَلُونَ
Qala wama AAilmee bimakanoo yaAAmaloon

Hausa
 
Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."

Ayah  26:113  الأية
إِنْ حِسَابُهُمْ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّي ۖ لَوْ تَشْعُرُونَ
In hisabuhum illa AAalarabbee law tashAAuroon

Hausa
 
"Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancẽwa."

Ayah  26:114  الأية
وَمَا أَنَا بِطَارِدِ الْمُؤْمِنِينَ
Wama ana bitaridialmu/mineen

Hausa
 
"Ban zama mai kõre mũminai ba."

Ayah  26:115  الأية
إِنْ أَنَا إِلَّا نَذِيرٌ مُّبِينٌ
In ana illa natheerunmubeen

Hausa
 
"Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa."

Ayah  26:116  الأية
قَالُوا لَئِن لَّمْ تَنتَهِ يَا نُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ الْمَرْجُومِينَ
Qaloo la-in lam tantahi yanoohu latakoonanna mina almarjoomeen

Hausa
 
Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"

Ayah  26:117  الأية
قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوْمِي كَذَّبُونِ
Qala rabbi inna qawmee kaththaboon

Hausa
 
Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."

Ayah  26:118  الأية
فَافْتَحْ بَيْنِي وَبَيْنَهُمْ فَتْحًا وَنَجِّنِي وَمَن مَّعِيَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ
Faftah baynee wabaynahum fathanwanajjinee waman maAAiya mina almu/mineen

Hausa
 
"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."

Ayah  26:119  الأية
فَأَنجَيْنَاهُ وَمَن مَّعَهُ فِي الْفُلْكِ الْمَشْحُونِ
Faanjaynahu waman maAAahu feealfulki almashhoon

Hausa
 
Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.

Ayah  26:120  الأية
ثُمَّ أَغْرَقْنَا بَعْدُ الْبَاقِينَ
Thumma aghraqna baAAdu albaqeen

Hausa
 
Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.

Ayah  26:121  الأية
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Inna fee thalika laayatan wamakana aktharuhum mu/mineen

Hausa
 
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

Ayah  26:122  الأية
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Wa-inna rabbaka lahuwa alAAazeezu arraheem

Hausa
 
Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.

Ayah  26:123  الأية
كَذَّبَتْ عَادٌ الْمُرْسَلِينَ
Kaththabat AAadun almursaleen

Hausa
 
Ãdãwa sun ƙaryata Manzanni.

Ayah  26:124  الأية
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ هُودٌ أَلَا تَتَّقُونَ
Ith qala lahum akhoohumhoodun ala tattaqoon

Hausa
 
A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

Ayah  26:125  الأية
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ
Innee lakum rasoolun ameen

Hausa
 
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."

Ayah  26:126  الأية
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Fattaqoo Allaha waateeAAoon

Hausa
 
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Ayah  26:127  الأية
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Wama as-alukum AAalayhi min ajrin inajriya illa AAala rabbi alAAalameen

Hausa
 
"Kuma bã ni tambayar wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba, fãce daga Ubangijin halittu."

Ayah  26:128  الأية
أَتَبْنُونَ بِكُلِّ رِيعٍ آيَةً تَعْبَثُونَ
Atabnoona bikulli reeAAin ayatantaAAbathoon

Hausa
 
"Shin, kunã yin ginin sitadiyo a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"

Ayah  26:129  الأية
وَتَتَّخِذُونَ مَصَانِعَ لَعَلَّكُمْ تَخْلُدُونَ
Watattakhithoona masaniAAalaAAallakum takhludoon

Hausa
 
"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?"

Ayah  26:130  الأية
وَإِذَا بَطَشْتُم بَطَشْتُمْ جَبَّارِينَ
Wa-itha batashtum batashtumjabbareen

Hausa
 
"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."

Ayah  26:131  الأية
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Fattaqoo Allaha waateeAAoon

Hausa
 
"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Ayah  26:132  الأية
وَاتَّقُوا الَّذِي أَمَدَّكُم بِمَا تَعْلَمُونَ
Wattaqoo allathee amaddakumbima taAAlamoon

Hausa
 
"Ku ji tsõron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani."

Ayah  26:133  الأية
أَمَدَّكُم بِأَنْعَامٍ وَبَنِينَ
Amaddakum bi-anAAamin wabaneen

Hausa
 
"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."

Ayah  26:134  الأية
وَجَنَّاتٍ وَعُيُونٍ
Wajannatin waAAuyoon

Hausa
 
"Da gõnaki da marẽmari."

Ayah  26:135  الأية
إِنِّي أَخَافُ عَلَيْكُمْ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍ
Innee akhafu AAalaykum AAathabayawmin AAatheem

Hausa
 
"Lalle ne nĩ, inã ji muku tsõron azãbar wani yini mai girma."

Ayah  26:136  الأية
قَالُوا سَوَاءٌ عَلَيْنَا أَوَعَظْتَ أَمْ لَمْ تَكُن مِّنَ الْوَاعِظِينَ
Qaloo sawaon AAalaynaawaAAathta am lam takun mina alwaAAitheen

Hausa
 
Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Kã yi wa'azi kõ ba ka kasance daga mãsu wa'azi ba."

Ayah  26:137  الأية
إِنْ هَٰذَا إِلَّا خُلُقُ الْأَوَّلِينَ
In hatha illa khuluqual-awwaleen

Hausa
 
"Wannan abu bai zamõ ba fãce hãlãyen mutãnen farko."

Ayah  26:138  الأية
وَمَا نَحْنُ بِمُعَذَّبِينَ
Wama nahnu bimuAAaththabeen

Hausa
 
"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."

Ayah  26:139  الأية
فَكَذَّبُوهُ فَأَهْلَكْنَاهُمْ ۗ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Fakaththaboohu faahlaknahuminna fee thalika laayatan wama kanaaktharuhum mu/mineen

Hausa
 
Sabõda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da sũ.Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

Ayah  26:140  الأية
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Wa-inna rabbaka lahuwa alAAazeezu arraheem

Hausa
 
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Ayah  26:141  الأية
كَذَّبَتْ ثَمُودُ الْمُرْسَلِينَ
Kaththabat thamoodu almursaleen

Hausa
 
Samũdãwa sun ƙaryata Manzanni.

Ayah  26:142  الأية
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ صَالِحٌ أَلَا تَتَّقُونَ
Ith qala lahum akhoohum salihunala tattaqoon

Hausa
 
A lõkacin da ɗan'uwansu Sãlihu ya ce: "Shin, bã zã ku bi Allah da taƙawa ba?"

Ayah  26:143  الأية
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ
Innee lakum rasoolun ameen

Hausa
 
"Lalle ne nĩ zuwã gare ku, Manzo ne, amintacce."

Ayah  26:144  الأية
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Fattaqoo Allaha waateeAAoon

Hausa
 
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.

Ayah  26:145  الأية
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Wama as-alukum AAalayhi min ajrin inajriya illa AAala rabbi alAAalameen

Hausa
 
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba fãce da a Ubangijin halittu."

Ayah  26:146  الأية
أَتُتْرَكُونَ فِي مَا هَاهُنَا آمِنِينَ
Atutrakoona fee ma hahunaamineen

Hausa
 
"Shin, anã barin ku a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"

Ayah  26:147  الأية
فِي جَنَّاتٍ وَعُيُونٍ
Fee jannatin waAAuyoon

Hausa
 
"A cikin gõnaki da marẽmari."

Ayah  26:148  الأية
وَزُرُوعٍ وَنَخْلٍ طَلْعُهَا هَضِيمٌ
WazurooAAin wanakhlin talAAuhahadeem

Hausa
 
"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi mãsu narkẽwa a ciki?"

Ayah  26:149  الأية
وَتَنْحِتُونَ مِنَ الْجِبَالِ بُيُوتًا فَارِهِينَ
Watanhitoona mina aljibalibuyootan fariheen

Hausa
 
"Kuma kunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, kunã mãsu alfãhari?"

Ayah  26:150  الأية
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Fattaqoo Allaha waateeAAoon

Hausa
 
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Ayah  26:151  الأية
وَلَا تُطِيعُوا أَمْرَ الْمُسْرِفِينَ
Wala tuteeAAoo amraalmusrifeen

Hausa
 
"Kada ku yi ɗã'ã ga umurnin maɓarnata."

Ayah  26:152  الأية
الَّذِينَ يُفْسِدُونَ فِي الْأَرْضِ وَلَا يُصْلِحُونَ
Allatheena yufsidoona fee al-ardiwala yuslihoon

Hausa
 
"Waɗanda suke yin ɓarna a cikin ƙasa, kuma bã su kyautatãwa."

Ayah  26:153  الأية
قَالُوا إِنَّمَا أَنتَ مِنَ الْمُسَحَّرِينَ
Qaloo innama anta mina almusahhareen

Hausa
 
Suka ce: "Kai daga mãsu sihiri kurum kake."

Ayah  26:154  الأية
مَا أَنتَ إِلَّا بَشَرٌ مِّثْلُنَا فَأْتِ بِآيَةٍ إِن كُنتَ مِنَ الصَّادِقِينَ
Ma anta illa basharun mithlunafa/ti bi-ayatin in kunta mina assadiqeena

Hausa
 
"Bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu. To, kã zo da wata ãyã idan kã kasance daga mãsu gaskiya."

Ayah  26:155  الأية
قَالَ هَٰذِهِ نَاقَةٌ لَّهَا شِرْبٌ وَلَكُمْ شِرْبُ يَوْمٍ مَّعْلُومٍ
Qala hathihi naqatunlaha shirbun walakum shirbu yawmin maAAloom

Hausa
 
Ya ce: "Wannan rãkuma ce tanã da shan yini, kuma kunã da shan yini sasanne."

Ayah  26:156  الأية
وَلَا تَمَسُّوهَا بِسُوءٍ فَيَأْخُذَكُمْ عَذَابُ يَوْمٍ عَظِيمٍ
Wala tamassooha bisoo-infaya/khuthakum AAathabu yawmin AAatheem

Hausa
 
"Kada ku shãfe ta da cũta har azãbar yini mai girmã ta shãfe ku."

Ayah  26:157  الأية
فَعَقَرُوهَا فَأَصْبَحُوا نَادِمِينَ
FaAAaqarooha faasbahoonadimeen

Hausa
 
Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.

Ayah  26:158  الأية
فَأَخَذَهُمُ الْعَذَابُ ۗ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Faakhathahumu alAAathabu innafee thalika laayatan wama kanaaktharuhum mu/mineen

Hausa
 
Sabõda haka azãba ta kãma su. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

Ayah  26:159  الأية
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Wa-inna rabbaka lahuwa alAAazeezu arraheem

Hausa
 
Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.

Ayah  26:160  الأية
كَذَّبَتْ قَوْمُ لُوطٍ الْمُرْسَلِينَ
Kaththabat qawmu lootinalmursaleen

Hausa
 
Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata Manzanni.

Ayah  26:161  الأية
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ لُوطٌ أَلَا تَتَّقُونَ
Ith qala lahum akhoohum lootunala tattaqoon

Hausa
 
A lõkacin da ɗan'uwansu, Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

Ayah  26:162  الأية
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ
Innee lakum rasoolun ameen

Hausa
 
"Lalle ne nĩ, zuwa gare ku, Manzõ ne, amintacce."

Ayah  26:163  الأية
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Fattaqoo Allaha waateeAAoon

Hausa
 
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Ayah  26:164  الأية
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Wama as-alukum AAalayhi min ajrin inajriya illa AAala rabbi alAAalameen

Hausa
 
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra, Ijãrãta ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

Ayah  26:165  الأية
أَتَأْتُونَ الذُّكْرَانَ مِنَ الْعَالَمِينَ
Ata/toona aththukranamina alAAalameen

Hausa
 
"Shin kunã jẽ wa maza daga cikin talikai?"

Ayah  26:166  الأية
وَتَذَرُونَ مَا خَلَقَ لَكُمْ رَبُّكُم مِّنْ أَزْوَاجِكُم ۚ بَلْ أَنتُمْ قَوْمٌ عَادُونَ
Watatharoona ma khalaqa lakumrabbukum min azwajikum bal antum qawmun AAadoon

Hausa
 
"Kuma kunã barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga mãtanku? Ã'a, ku mutãne ne mãsu ƙẽtarẽwa!"

Ayah  26:167  الأية
قَالُوا لَئِن لَّمْ تَنتَهِ يَا لُوطُ لَتَكُونَنَّ مِنَ الْمُخْرَجِينَ
Qaloo la-in lam tantahi yalootu latakoonanna mina almukhrajeen

Hausa
 
Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."

Ayah  26:168  الأية
قَالَ إِنِّي لِعَمَلِكُم مِّنَ الْقَالِينَ
Qala innee liAAamalikum mina alqaleen

Hausa
 
Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa."

Ayah  26:169  الأية
رَبِّ نَجِّنِي وَأَهْلِي مِمَّا يَعْمَلُونَ
Rabbi najjinee waahlee mimmayaAAmaloon

Hausa
 
"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."

Ayah  26:170  الأية
فَنَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ أَجْمَعِينَ
Fanajjaynahu waahlahu ajmaAAeen

Hausa
 
Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.

Ayah  26:171  الأية
إِلَّا عَجُوزًا فِي الْغَابِرِينَ
Illa AAajoozan fee alghabireen

Hausa
 
Fãce wata tsõhuwa a cikin mãsu wanzuwa.

Ayah  26:172  الأية
ثُمَّ دَمَّرْنَا الْآخَرِينَ
Thumma dammarna al-akhareen

Hausa
 
Sa'an nan kuma Muka darkãke wasu.

Ayah  26:173  الأية
وَأَمْطَرْنَا عَلَيْهِم مَّطَرًا ۖ فَسَاءَ مَطَرُ الْمُنذَرِينَ
Waamtarna AAalayhim mataranfasaa mataru almunthareen

Hausa
 
Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana.

Ayah  26:174  الأية
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Inna fee thalika laayatan wamakana aktharuhum mu/mineen

Hausa
 
Lalle ne ga wannan, akwai ãyã, kuma mafi yawansu bã su kasance mãsu ĩmãni ba.

Ayah  26:175  الأية
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Wa-inna rabbaka lahuwa alAAazeezu arraheem

Hausa
 
Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Ayah  26:176  الأية
كَذَّبَ أَصْحَابُ الْأَيْكَةِ الْمُرْسَلِينَ
Kaththaba as-habual-aykati almursaleen

Hausa
 
Ma'abũta ƙunci sun ƙaryata Manzanni.

Ayah  26:177  الأية
إِذْ قَالَ لَهُمْ شُعَيْبٌ أَلَا تَتَّقُونَ
Ith qala lahum shuAAaybun alatattaqoon

Hausa
 
A lõkacin da Shu'aibu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

Ayah  26:178  الأية
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ
Innee lakum rasoolun ameen

Hausa
 
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce."

Ayah  26:179  الأية
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Fattaqoo Allaha waateeAAoon

Hausa
 
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."

Ayah  26:180  الأية
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Wama as-alukum AAalayhi min ajrin inajriya illa AAala rabbi alAAalameen

Hausa
 
"Kuma ba ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

Ayah  26:181  الأية
أَوْفُوا الْكَيْلَ وَلَا تَكُونُوا مِنَ الْمُخْسِرِينَ
Awfoo alkayla wala takoonoo minaalmukhsireen

Hausa
 
"Ku cika mũdu, kuma kada ku kasance daga mãsu sanyãwar hasãra (ga mutãne)."

Ayah  26:182  الأية
وَزِنُوا بِالْقِسْطَاسِ الْمُسْتَقِيمِ
Wazinoo bilqistasialmustaqeem

Hausa
 
"Kuma ku yi awo da sikẽli daidaitacce."

Ayah  26:183  الأية
وَلَا تَبْخَسُوا النَّاسَ أَشْيَاءَهُمْ وَلَا تَعْثَوْا فِي الْأَرْضِ مُفْسِدِينَ
Wala tabkhasoo annasaashyaahum wala taAAthaw fee al-ardimufsideen

Hausa
 
"Kuma kada ku nakasa wa mutãne abũbuwansu kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa kuna mãsu ɓarna."

Ayah  26:184  الأية
وَاتَّقُوا الَّذِي خَلَقَكُمْ وَالْجِبِلَّةَ الْأَوَّلِينَ
Wattaqoo allathee khalaqakumwaljibillata al-awwaleen

Hausa
 
"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."

Ayah  26:185  الأية
قَالُوا إِنَّمَا أَنتَ مِنَ الْمُسَحَّرِينَ
Qaloo innama anta mina almusahhareen

Hausa
 
Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne."

Ayah  26:186  الأية
وَمَا أَنتَ إِلَّا بَشَرٌ مِّثْلُنَا وَإِن نَّظُنُّكَ لَمِنَ الْكَاذِبِينَ
Wama anta illa basharunmithluna wa-in nathunnuka lamina alkathibeen

Hausa
 
"Kuma bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu kuma lalle ne munã zaton ka, haƙĩƙa, daga maƙaryata."

Ayah  26:187  الأية
فَأَسْقِطْ عَلَيْنَا كِسَفًا مِّنَ السَّمَاءِ إِن كُنتَ مِنَ الصَّادِقِينَ
Faasqit AAalayna kisafan minaassama-i in kunta mina assadiqeen

Hausa
 
"To ka jẽfo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga mãsu gaskiya."

Ayah  26:188  الأية
قَالَ رَبِّي أَعْلَمُ بِمَا تَعْمَلُونَ
Qala rabbee aAAlamu bimataAAmaloon

Hausa
 
Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa."

Ayah  26:189  الأية
فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَهُمْ عَذَابُ يَوْمِ الظُّلَّةِ ۚ إِنَّهُ كَانَ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍ
Fakaththaboohu faakhathahumAAathabu yawmi aththullati innahu kanaAAathaba yawmin AAatheem

Hausa
 
Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma.

Ayah  26:190  الأية
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Inna fee thalika laayatan wamakana aktharuhum mu/mineen

Hausa
 
Lalle a cikin wancan haƙĩka akwai ãya, amma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

Ayah  26:191  الأية
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Wa-inna rabbaka lahuwa alAAazeezu arraheem

Hausa
 
Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Ayah  26:192  الأية
وَإِنَّهُ لَتَنزِيلُ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Wa-innahu latanzeelu rabbi alAAalameen

Hausa
 
Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.

Ayah  26:193  الأية
نَزَلَ بِهِ الرُّوحُ الْأَمِينُ
Nazala bihi arroohu al-ameen

Hausa
 
Rũhi amintacce ne ya sauka da shi.

Ayah  26:194  الأية
عَلَىٰ قَلْبِكَ لِتَكُونَ مِنَ الْمُنذِرِينَ
AAala qalbika litakoona mina almunthireen

Hausa
 
A kan zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.

Ayah  26:195  الأية
بِلِسَانٍ عَرَبِيٍّ مُّبِينٍ
Bilisanin AAarabiyyin mubeen

Hausa
 
Da harshe na Larabci mai bayãni.

Ayah  26:196  الأية
وَإِنَّهُ لَفِي زُبُرِ الْأَوَّلِينَ
Wa-innahu lafee zuburi al-awwaleen

Hausa
 
Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.

Ayah  26:197  الأية
أَوَلَمْ يَكُن لَّهُمْ آيَةً أَن يَعْلَمَهُ عُلَمَاءُ بَنِي إِسْرَائِيلَ
Awa lam yakun lahum ayatan anyaAAlamahu AAulamao banee isra-eel

Hausa
 
Ashe, bai kasance ãyã ba a gare su, ya zama Mãlaman Banĩ Isrã'ĩla sun san shi?

Ayah  26:198  الأية
وَلَوْ نَزَّلْنَاهُ عَلَىٰ بَعْضِ الْأَعْجَمِينَ
Walaw nazzalnahu AAala baAAdial-aAAjameen

Hausa
 
Kuma dã mun saukar da shi a kan sãshen Ajamãwa,

Ayah  26:199  الأية
فَقَرَأَهُ عَلَيْهِم مَّا كَانُوا بِهِ مُؤْمِنِينَ
Faqaraahu AAalayhim ma kanoobihi mu/mineen

Hausa
 
Ya karanta shi a kansu, ba su kasance sabõda shi mãsu ĩmãni ba.

Ayah  26:200  الأية
كَذَٰلِكَ سَلَكْنَاهُ فِي قُلُوبِ الْمُجْرِمِينَ
Kathalika salaknahu feequloobi almujrimeen

Hausa
 
Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.

Ayah  26:201  الأية
لَا يُؤْمِنُونَ بِهِ حَتَّىٰ يَرَوُا الْعَذَابَ الْأَلِيمَ
La yu/minoona bihi hattayarawoo alAAathaba al-aleem

Hausa
 
Bã zã su yi ĩmãni da shĩ ba sai sun ga azãbar nan mai raɗadi.

Ayah  26:202  الأية
فَيَأْتِيَهُم بَغْتَةً وَهُمْ لَا يَشْعُرُونَ
Faya/tiyahum baghtatan wahum layashAAuroon

Hausa
 
Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba.

Ayah  26:203  الأية
فَيَقُولُوا هَلْ نَحْنُ مُنظَرُونَ
Fayaqooloo hal nahnu muntharoon

Hausa
 
Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?"

Ayah  26:204  الأية
أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ
AfabiAAathabina yastaAAjiloon

Hausa
 
Ashe, to, da azãbarMu suke nẽman gaggãwa?

Ayah  26:205  الأية
أَفَرَأَيْتَ إِن مَّتَّعْنَاهُمْ سِنِينَ
Afaraayta in mattaAAnahum sineen

Hausa
 
Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,

Ayah  26:206  الأية
ثُمَّ جَاءَهُم مَّا كَانُوا يُوعَدُونَ
Thumma jaahum ma kanooyooAAadoon

Hausa
 
Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,

Ayah  26:207  الأية
مَا أَغْنَىٰ عَنْهُم مَّا كَانُوا يُمَتَّعُونَ
Ma aghna AAanhum ma kanooyumattaAAoon

Hausa
 
Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare su.

Ayah  26:208  الأية
وَمَا أَهْلَكْنَا مِن قَرْيَةٍ إِلَّا لَهَا مُنذِرُونَ
Wama ahlakna min qaryatin illalaha munthiroon

Hausa
 
Kuma bã Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da mãsu gargaɗi.

Ayah  26:209  الأية
ذِكْرَىٰ وَمَا كُنَّا ظَالِمِينَ
Thikra wama kunnathalimeen

Hausa
 
Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba.

Ayah  26:210  الأية
وَمَا تَنَزَّلَتْ بِهِ الشَّيَاطِينُ
Wama tanazzalat bihi ashshayateen

Hausa
 
Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.

Ayah  26:211  الأية
وَمَا يَنبَغِي لَهُمْ وَمَا يَسْتَطِيعُونَ
Wama yanbaghee lahum wamayastateeAAoon

Hausa
 
Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.

Ayah  26:212  الأية
إِنَّهُمْ عَنِ السَّمْعِ لَمَعْزُولُونَ
Innahum AAani assamAAilamaAAzooloona

Hausa
 
Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.

Ayah  26:213  الأية
فَلَا تَدْعُ مَعَ اللهِ إِلَٰهًا آخَرَ فَتَكُونَ مِنَ الْمُعَذَّبِينَ
Fala tadAAu maAAa Allahi ilahanakhara fatakoona mina almuAAaththabeen

Hausa
 
Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.

Ayah  26:214  الأية
وَأَنذِرْ عَشِيرَتَكَ الْأَقْرَبِينَ
Waanthir AAasheerataka al-aqrabeen

Hausa
 
Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.

Ayah  26:215  الأية
وَاخْفِضْ جَنَاحَكَ لِمَنِ اتَّبَعَكَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ
Wakhfid janahakalimani ittabaAAaka mina almu/mineen

Hausa
 
Kuma ka sassauta fikãfikanka ga wanda ya bĩ ka daga mũminai.

Ayah  26:216  الأية
فَإِنْ عَصَوْكَ فَقُلْ إِنِّي بَرِيءٌ مِّمَّا تَعْمَلُونَ
Fa-in AAasawka faqul innee baree-onmimma taAAmaloon

Hausa
 
Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."

Ayah  26:217  الأية
وَتَوَكَّلْ عَلَى الْعَزِيزِ الرَّحِيمِ
Watawakkal AAala alAAazeezi arraheem

Hausa
 
Kuma ka dõgara ga Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Ayah  26:218  الأية
الَّذِي يَرَاكَ حِينَ تَقُومُ
Allathee yaraka heenataqoom

Hausa
 
Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye.

Ayah  26:219  الأية
وَتَقَلُّبَكَ فِي السَّاجِدِينَ
Wataqallubaka fee assajideen

Hausa
 
Da jujjuyãwarka a cikin mãsu yin sujada.

Ayah  26:220  الأية
إِنَّهُ هُوَ السَّمِيعُ الْعَلِيمُ
Innahu huwa assameeAAu alAAaleem

Hausa
 
Lalle Shi, Shi ne Mai ji,Masani.

Ayah  26:221  الأية
هَلْ أُنَبِّئُكُمْ عَلَىٰ مَن تَنَزَّلُ الشَّيَاطِينُ
Hal onabbi-okum AAala man tanazzaluashshayateen

Hausa
 
Shin, (kunã so) in gaya muku a kan wanda Shaiɗãnnu kan sauka?

Ayah  26:222  الأية
تَنَزَّلُ عَلَىٰ كُلِّ أَفَّاكٍ أَثِيمٍ
Tanazzalu AAala kulli affakinatheem

Hausa
 
Sukan sauka a kan dukkan maƙaryaci, mai zunubi.

Ayah  26:223  الأية
يُلْقُونَ السَّمْعَ وَأَكْثَرُهُمْ كَاذِبُونَ
Yulqoona assamAAa waaktharuhum kathiboon

Hausa
 
Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.

Ayah  26:224  الأية
وَالشُّعَرَاءُ يَتَّبِعُهُمُ الْغَاوُونَ
WashshuAAaraoyattabiAAuhumu alghawoon

Hausa
 
Kuma mawãƙa halakakku ne ke bin su.

Ayah  26:225  الأية
أَلَمْ تَرَ أَنَّهُمْ فِي كُلِّ وَادٍ يَهِيمُونَ
Alam tara annahum fee kulli wadinyaheemoon

Hausa
 
Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?

Ayah  26:226  الأية
وَأَنَّهُمْ يَقُولُونَ مَا لَا يَفْعَلُونَ
Waannahum yaqooloona ma layafAAaloon

Hausa
 
Kuma lalle ne, sũ, sunã faɗin abin da bã su aikatãwa?

Ayah  26:227  الأية
إِلَّا الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ وَذَكَرُوا اللهَ كَثِيرًا وَانتَصَرُوا مِن بَعْدِ مَا ظُلِمُوا ۗ وَسَيَعْلَمُ الَّذِينَ ظَلَمُوا أَيَّ مُنقَلَبٍ يَنقَلِبُونَ
Illa allatheena amanoowaAAamiloo assalihati wathakaroo Allahakatheeran wantasaroo min baAAdi ma thulimoowasayaAAlamu allatheena thalamoo ayyamunqalabin yanqaliboon

Hausa
 
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka ambaci Allah da yawa, kuma suka rãma zãlunci, daga bãyan an zãlunce su. Kuma waɗanda suka yi zãlunci, zã su sani a wace majũya suke jũyãwa.





© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us