Prev  

81. Surah At-Takwîr سورة التكوير

  Next  




1st Ayah  1  الأية ١الأولي
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
إِذَا الشَّمْسُ كُوِّرَتْ
Itha ashshamsu kuwwirat

Hausa
 
Idan rãna aka shafe haskenta

Ayah  81:2  الأية
وَإِذَا النُّجُومُ انكَدَرَتْ
Wa-itha annujoomu inkadarat

Hausa
 
Kuma idan taurãri suka gurɓãce (wani ya shiga a cikin wani).

Ayah  81:3  الأية
وَإِذَا الْجِبَالُ سُيِّرَتْ
Wa-itha aljibalu suyyirat

Hausa
 
Kuma idan duwãtsu aka tafiyar da su.

Ayah  81:4  الأية
وَإِذَا الْعِشَارُ عُطِّلَتْ
Wa-itha alAAisharu AAuttilat

Hausa
 
Kuma idan rãƙuma mãsu cikunna aka sakẽ su wãwai, bã ga kõwa ba.

Ayah  81:5  الأية
وَإِذَا الْوُحُوشُ حُشِرَتْ
Wa-itha alwuhooshu hushirat

Hausa
 
Kuma idan dabbõbin dãji aka tattara su.

Ayah  81:6  الأية
وَإِذَا الْبِحَارُ سُجِّرَتْ
Wa-itha albiharu sujjirat

Hausa
 
Kuma idan tẽkuna aka mayar da su wuta.

Ayah  81:7  الأية
وَإِذَا النُّفُوسُ زُوِّجَتْ
Wa-itha annufoosu zuwwijat

Hausa
 
Kuma idan rãyuka aka haɗa su da jikunkunansu.

Ayah  81:8  الأية
وَإِذَا الْمَوْءُودَةُ سُئِلَتْ
Wa-itha almawoodatu su-ilat

Hausa
 
Kuma idan wadda aka turbuɗe ta da rai aka tambaye ta.

Ayah  81:9  الأية
بِأَيِّ ذَنبٍ قُتِلَتْ
Bi-ayyi thanbin qutilat

Hausa
 
"Sabõda wane laifi ne aka kashe ta?"

Ayah  81:10  الأية
وَإِذَا الصُّحُفُ نُشِرَتْ
Wa-itha assuhufunushirat

Hausa
 
Idan takardun ayyuka aka wãtsa su (ga mãsu su).

Ayah  81:11  الأية
وَإِذَا السَّمَاءُ كُشِطَتْ
Wa-itha assamao kushitat

Hausa
 
Kuma idan sama aka fẽɗe ta.

Ayah  81:12  الأية
وَإِذَا الْجَحِيمُ سُعِّرَتْ
Wa-itha aljaheemu suAAAAirat

Hausa
 
Kuma idan Jahĩm aka hũra ta

Ayah  81:13  الأية
وَإِذَا الْجَنَّةُ أُزْلِفَتْ
Wa-itha aljannatu ozlifat

Hausa
 
Kuma idan Aljanna aka kusantar da ita.

Ayah  81:14  الأية
عَلِمَتْ نَفْسٌ مَّا أَحْضَرَتْ
AAalimat nafsun ma ahdarat

Hausa
 
Rai ya san abin da ya halartar (a rãnar nan).

Ayah  81:15  الأية
فَلَا أُقْسِمُ بِالْخُنَّسِ
Fala oqsimu bilkhunnas

Hausa
 
To, ba sai Na yi rantsuwa da taurãri matafã ba.

Ayah  81:16  الأية
الْجَوَارِ الْكُنَّسِ
Aljawari alkunnas

Hausa
 
Mãsu gudu suna ɓũya.

Ayah  81:17  الأية
وَاللَّيْلِ إِذَا عَسْعَسَ
Wallayli itha AAasAAas

Hausa
 
Da dare idan ya bãyar da bãya.

Ayah  81:18  الأية
وَالصُّبْحِ إِذَا تَنَفَّسَ
Wassubhi ithatanaffas

Hausa
 
Da sãfiya idan ta yi lumfashi.

Ayah  81:19  الأية
إِنَّهُ لَقَوْلُ رَسُولٍ كَرِيمٍ
Innahu laqawlu rasoolin kareem

Hausa
 
Lalle ne shi (Alƙur'ãni) haƙƙan, maganar wani manzon (Allah) ne mai girma ga Allah.

Ayah  81:20  الأية
ذِي قُوَّةٍ عِندَ ذِي الْعَرْشِ مَكِينٍ
Thee quwwatin AAinda theealAAarshi makeen

Hausa
 
Mai ƙarfi, mai daraja a wurin Mai Al'arshi.

Ayah  81:21  الأية
مُّطَاعٍ ثَمَّ أَمِينٍ
MutaAAin thamma ameen

Hausa
 
Wanda ake yi wa ɗã'a (wato shugaban malã'iku) ne a can, amintacce.

Ayah  81:22  الأية
وَمَا صَاحِبُكُم بِمَجْنُونٍ
Wama sahibukum bimajnoon

Hausa
 
Kuma abokinku ba mahaukaci ba ne.

Ayah  81:23  الأية
وَلَقَدْ رَآهُ بِالْأُفُقِ الْمُبِينِ
Walaqad raahu bilofuqialmubeen

Hausa
 
Kuma lalle ne, yã gan shi a cikin sararin sama mabayyani.

Ayah  81:24  الأية
وَمَا هُوَ عَلَى الْغَيْبِ بِضَنِينٍ
Wama huwa AAala alghaybi bidaneen

Hausa
 
Kuma shi, ga gaibi bã mai rowa ba ne.

Ayah  81:25  الأية
وَمَا هُوَ بِقَوْلِ شَيْطَانٍ رَّجِيمٍ
Wama huwa biqawli shaytaninrajeem

Hausa
 
Kuma shi (Alƙur'ani) bã maganar shaiɗani, wanda aka la'ana, ba ce.

Ayah  81:26  الأية
فَأَيْنَ تَذْهَبُونَ
Faayna tathhaboon

Hausa
 
Shin, a inã zã ku tafi?

Ayah  81:27  الأية
إِنْ هُوَ إِلَّا ذِكْرٌ لِّلْعَالَمِينَ
In huwa illa thikrun lilAAalameen

Hausa
 
Lalle ne shi (Alƙur'ãni), bã kõme ba ne fãce gargaɗi ga talikai.

Ayah  81:28  الأية
لِمَن شَاءَ مِنكُمْ أَن يَسْتَقِيمَ
Liman shaa minkum an yastaqeem

Hausa
 
Ga wanda ya so, daga cikinku, ya shiryu.

Ayah  81:29  الأية
وَمَا تَشَاءُونَ إِلَّا أَن يَشَاءَ اللهُ رَبُّ الْعَالَمِينَ
Wama tashaoona illa anyashaa Allahu rabbu alAAalameen

Hausa
 
Kuma bã zã ku so ba sai idan Allah Ubangijin halitta Yã yarda.





© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us