Prev
84. Surah Al-Inshiqâq سورة الإنشقاق
Next
1st Ayah 1 الأية ١الأوليبِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
إِذَا السَّمَاءُ انشَقَّتْ
Itha assamao inshaqqat
Hausa
Idan sama ta kẽce,
|
Ayah 84:2 الأية
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
Waathinat lirabbiha wahuqqat
Hausa
Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,
|
Ayah 84:3 الأية
وَإِذَا الْأَرْضُ مُدَّتْ
Wa-itha al-ardu muddat
Hausa
Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,
|
Ayah 84:4 الأية
وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ
Waalqat ma feeha watakhallat
Hausa
Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.
|
Ayah 84:5 الأية
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
Waathinat lirabbiha wahuqqat
Hausa
Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,
|
Ayah 84:6 الأية
يَا أَيُّهَا الْإِنسَانُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدْحًا فَمُلَاقِيهِ
Ya ayyuha al-insanuinnaka kadihun ila rabbika kadhanfamulaqeeh
Hausa
Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala
mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.
|
Ayah 84:7 الأية
فَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِيَمِينِهِ
Faama man ootiya kitabahubiyameenih
Hausa
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.
|
Ayah 84:8 الأية
فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًا يَسِيرًا
Fasawfa yuhasabu hisabanyaseera
Hausa
To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.
|
Ayah 84:9 الأية
وَيَنقَلِبُ إِلَىٰ أَهْلِهِ مَسْرُورًا
Wayanqalibu ila ahlihi masroora
Hausa
Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.
|
Ayah 84:10 الأية
وَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ وَرَاءَ ظَهْرِهِ
Waamma man ootiya kitabahu waraathahrih
Hausa
Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.
|
Ayah 84:11 الأية
فَسَوْفَ يَدْعُو ثُبُورًا
Fasawfa yadAAoo thuboora
Hausa
To, zã shi dinga kiran halaka!
|
Ayah 84:12 الأية
وَيَصْلَىٰ سَعِيرًا
Wayasla saAAeera
Hausa
Kuma ya shiga sa'ĩr.
|
Ayah 84:13 الأية
إِنَّهُ كَانَ فِي أَهْلِهِ مَسْرُورًا
Innahu kana fee ahlihi masroora
Hausa
Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.
|
Ayah 84:14 الأية
إِنَّهُ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ
Innahu thanna an lan yahoor
Hausa
Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.
|
Ayah 84:15 الأية
بَلَىٰ إِنَّ رَبَّهُ كَانَ بِهِ بَصِيرًا
Bala inna rabbahu kana bihi baseera
Hausa
Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.
|
Ayah 84:16 الأية
فَلَا أُقْسِمُ بِالشَّفَقِ
Fala oqsimu bishshafaq
Hausa
To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.
|
Ayah 84:17 الأية
وَاللَّيْلِ وَمَا وَسَقَ
Wallayli wama wasaq
Hausa
Da dare, da abin da ya ƙunsa.
|
Ayah 84:18 الأية
وَالْقَمَرِ إِذَا اتَّسَقَ
Walqamari itha ittasaq
Hausa
Da watã idan (haskensa) ya cika.
|
Ayah 84:19 الأية
لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍ
Latarkabunna tabaqan AAan tabaq
Hausa
Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.
|
Ayah 84:20 الأية
فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ
Fama lahum la yu/minoon
Hausa
To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?
|
Ayah 84:21 الأية
وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ الْقُرْآنُ لَا يَسْجُدُونَ ۩
Wa-itha quri-a AAalayhimu alqur-anula yasjudoon
Hausa
Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?
|
Ayah 84:22 الأية
بَلِ الَّذِينَ كَفَرُوا يُكَذِّبُونَ
Bali allatheena kafaroo yukaththiboon
Hausa
Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.
|
Ayah 84:23 الأية
وَاللهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ
Wallahu aAAlamu bimayooAAoon
Hausa
Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.
|
Ayah 84:24 الأية
فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ
Fabashshirhum biAAathabin aleem
Hausa
Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.
|
Ayah 84:25 الأية
إِلَّا الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍ
Illa allatheena amanoowaAAamiloo assalihati lahum ajrun ghayrumamnoon
Hausa
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako
wanda bã ya yankẽwa.
|
©
EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us
|
|