Prev  

84. Surah Al-Inshiqâq سورة الإنشقاق

  Next  



1st Ayah  1  الأية ١الأولي
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
إِذَا السَّمَاءُ انشَقَّتْ
Itha assamao inshaqqat

Hausa
 
Idan sama ta kẽce,

Ayah  84:2  الأية
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
Waathinat lirabbiha wahuqqat

Hausa
 
Ta saurari Ubangijinta, kuma aka wajabta mata yin saurãron,

Ayah  84:3  الأية
وَإِذَا الْأَرْضُ مُدَّتْ
Wa-itha al-ardu muddat

Hausa
 
Kuma idan ƙasã aka mĩƙe ta,

Ayah  84:4  الأية
وَأَلْقَتْ مَا فِيهَا وَتَخَلَّتْ
Waalqat ma feeha watakhallat

Hausa
 
Kuma ta jẽfar da abin da yake a cikinta, tã wõfinta daga kõme.

Ayah  84:5  الأية
وَأَذِنَتْ لِرَبِّهَا وَحُقَّتْ
Waathinat lirabbiha wahuqqat

Hausa
 
Kuma ta saurãri Ubangijinta, aka wajabta mata yin saurãren,

Ayah  84:6  الأية
يَا أَيُّهَا الْإِنسَانُ إِنَّكَ كَادِحٌ إِلَىٰ رَبِّكَ كَدْحًا فَمُلَاقِيهِ
Ya ayyuha al-insanuinnaka kadihun ila rabbika kadhanfamulaqeeh

Hausa
 
Ya kai mutum! Lalle ne kai mai aikin wahal da kai ne zuwa ga Ubangijinka, wahala mai tsanani, To, kai mai haɗuwa da Shi ne.

Ayah  84:7  الأية
فَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ بِيَمِينِهِ
Faama man ootiya kitabahubiyameenih

Hausa
 
To, amma wanda aka bai wa littãfinsa da damansa.

Ayah  84:8  الأية
فَسَوْفَ يُحَاسَبُ حِسَابًا يَسِيرًا
Fasawfa yuhasabu hisabanyaseera

Hausa
 
To, za a yi masa hisãbi, hisãbi mai sauƙi.

Ayah  84:9  الأية
وَيَنقَلِبُ إِلَىٰ أَهْلِهِ مَسْرُورًا
Wayanqalibu ila ahlihi masroora

Hausa
 
Kuma ya jũya zuwa ga iyãlinsa (a cikin Aljanna), yanã mai raha.

Ayah  84:10  الأية
وَأَمَّا مَنْ أُوتِيَ كِتَابَهُ وَرَاءَ ظَهْرِهِ
Waamma man ootiya kitabahu waraathahrih

Hausa
 
Kuma amma wanda aka bai wa littãfinsa, daga wajen bãyansa.

Ayah  84:11  الأية
فَسَوْفَ يَدْعُو ثُبُورًا
Fasawfa yadAAoo thuboora

Hausa
 
To, zã shi dinga kiran halaka!

Ayah  84:12  الأية
وَيَصْلَىٰ سَعِيرًا
Wayasla saAAeera

Hausa
 
Kuma ya shiga sa'ĩr.

Ayah  84:13  الأية
إِنَّهُ كَانَ فِي أَهْلِهِ مَسْرُورًا
Innahu kana fee ahlihi masroora

Hausa
 
Lal1e ne shi, yã kasance (a dũniya) cikin iyãlinsa yanã mai raha.

Ayah  84:14  الأية
إِنَّهُ ظَنَّ أَن لَّن يَحُورَ
Innahu thanna an lan yahoor

Hausa
 
Lalle ne yã yi zaton bã zai kõmo ba.

Ayah  84:15  الأية
بَلَىٰ إِنَّ رَبَّهُ كَانَ بِهِ بَصِيرًا
Bala inna rabbahu kana bihi baseera

Hausa
 
Na'am! Lalle ne, Ubangijinsa Ya kasance Mai gani gare shi.

Ayah  84:16  الأية
فَلَا أُقْسِمُ بِالشَّفَقِ
Fala oqsimu bishshafaq

Hausa
 
To, ba sai Nã rantse da shafaƙi ba.

Ayah  84:17  الأية
وَاللَّيْلِ وَمَا وَسَقَ
Wallayli wama wasaq

Hausa
 
Da dare, da abin da ya ƙunsa.

Ayah  84:18  الأية
وَالْقَمَرِ إِذَا اتَّسَقَ
Walqamari itha ittasaq

Hausa
 
Da watã idan (haskensa) ya cika.

Ayah  84:19  الأية
لَتَرْكَبُنَّ طَبَقًا عَن طَبَقٍ
Latarkabunna tabaqan AAan tabaq

Hausa
 
Lalle ne kunã hawan wani hãli daga wani hãli.

Ayah  84:20  الأية
فَمَا لَهُمْ لَا يُؤْمِنُونَ
Fama lahum la yu/minoon

Hausa
 
To, mẽ ya sãme su, ba su yin ĩmãni?

Ayah  84:21  الأية
وَإِذَا قُرِئَ عَلَيْهِمُ الْقُرْآنُ لَا يَسْجُدُونَ ۩
Wa-itha quri-a AAalayhimu alqur-anula yasjudoon

Hausa
 
Kuma idan an karanta Alkur'ãni a kansu, bã su yin tawãli'u?

Ayah  84:22  الأية
بَلِ الَّذِينَ كَفَرُوا يُكَذِّبُونَ
Bali allatheena kafaroo yukaththiboon

Hausa
 
Ba haka ba! waɗanda suka kãfirta, sai ƙaryatãwa suke yi.

Ayah  84:23  الأية
وَاللهُ أَعْلَمُ بِمَا يُوعُونَ
Wallahu aAAlamu bimayooAAoon

Hausa
 
Alhãli Allah Shĩ ne Mafi sani ga abin a suke tãrãwa.

Ayah  84:24  الأية
فَبَشِّرْهُم بِعَذَابٍ أَلِيمٍ
Fabashshirhum biAAathabin aleem

Hausa
 
Saboda haka, ka yi musu bushãra da azãba mai raɗaɗi.

Ayah  84:25  الأية
إِلَّا الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ لَهُمْ أَجْرٌ غَيْرُ مَمْنُونٍ
Illa allatheena amanoowaAAamiloo assalihati lahum ajrun ghayrumamnoon

Hausa
 
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni, suka aikata ayyukan ƙwarai, sunã da wani sakamako wanda bã ya yankẽwa. 




© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us