Prev  

87. Surah Al-A'lâ سورة الأعلى

  Next  



1st Ayah  1  الأية ١الأولي
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
سَبِّحِ اسْمَ رَبِّكَ الْأَعْلَى
Sabbihi isma rabbika al-aAAla

Hausa
 
Ka tsarkake sũnan Ubangijinka Mafi ɗaukaka.

Ayah  87:2  الأية
الَّذِي خَلَقَ فَسَوَّىٰ
Allathee khalaqa fasawwa

Hausa
 
Wanda Yã yi halitta sa'an nan Ya daidaita abin halittar.

Ayah  87:3  الأية
وَالَّذِي قَدَّرَ فَهَدَىٰ
Wallathee qaddara fahada

Hausa
 
Kuma Wanda Ya ƙaddara (abin da Ya so) sannan Ya shiryar,(da mutum ga hanyar alhẽri da ta sharri).

Ayah  87:4  الأية
وَالَّذِي أَخْرَجَ الْمَرْعَىٰ
Wallathee akhraja almarAAa

Hausa
 
Kuma Wanda Ya fitar da makiyãyã.

Ayah  87:5  الأية
فَجَعَلَهُ غُثَاءً أَحْوَىٰ
FajaAAalahu ghuthaan ahwa

Hausa
 
Sa'an nan Ya mayar da ita ƙeƙasassa, baƙa.

Ayah  87:6  الأية
سَنُقْرِئُكَ فَلَا تَنسَىٰ
Sanuqri-oka fala tansa

Hausa
 
Za mu karantar da kai (Alƙur'ãni) sabõda haka bã zã ka mantã (shi) ba.

Ayah  87:7  الأية
إِلَّا مَا شَاءَ اللهُ ۚ إِنَّهُ يَعْلَمُ الْجَهْرَ وَمَا يَخْفَىٰ
Illa ma shaa Allahuinnahu yaAAlamu aljahra wama yakhfa

Hausa
 
Fãce abin da Allah Ya so, lalle ne Shi (Allah) Ya san bayyane da abin da yake bõye.

Ayah  87:8  الأية
وَنُيَسِّرُكَ لِلْيُسْرَىٰ
Wanuyassiruka lilyusra

Hausa
 
Kuma za Mu sauƙaƙe maka (al'amari) zuwa ga (Shari'a) mai sauƙi.

Ayah  87:9  الأية
فَذَكِّرْ إِن نَّفَعَتِ الذِّكْرَىٰ
Fathakkir in nafaAAati aththikra

Hausa
 
Sabõda baka, ka tunãtar, idan tunatarwa zã ta yi amfãni.

Ayah  87:10  الأية
سَيَذَّكَّرُ مَن يَخْشَىٰ
Sayaththakkaru man yakhsha

Hausa
 
Wanda yake tsõron (Allah) Zai tuna.

Ayah  87:11  الأية
وَيَتَجَنَّبُهَا الْأَشْقَى
Wayatajannabuha al-ashqa

Hausa
 
Kuma shaƙiyyi, zai nisanceta,

Ayah  87:12  الأية
الَّذِي يَصْلَى النَّارَ الْكُبْرَىٰ
Allathee yasla annaraalkubra

Hausa
 
Wanda zai shiga wutar da tã fi girma.

Ayah  87:13  الأية
ثُمَّ لَا يَمُوتُ فِيهَا وَلَا يَحْيَىٰ
Thumma la yamootu feeha walayahya

Hausa
 
Sa'an nan bã zai mutu ba a cikinta, kuma bã zai rãyu ba.

Ayah  87:14  الأية
قَدْ أَفْلَحَ مَن تَزَكَّىٰ
Qad aflaha man tazakka

Hausa
 
Lalle ne wanda ya tsarkaka (da ĩmãni) yã sãmu babban rabo.

Ayah  87:15  الأية
وَذَكَرَ اسْمَ رَبِّهِ فَصَلَّىٰ
Wathakara isma rabbihi fasalla

Hausa
 
Kuma ya ambaci sũnan Ubangijinsa, sa'an nan yã yi salla.

Ayah  87:16  الأية
بَلْ تُؤْثِرُونَ الْحَيَاةَ الدُّنْيَا
Bal tu/thiroona alhayata addunya

Hausa
 
Ba haka ba! Kunã zãɓin rãyuwa ta kusa dũniya.

Ayah  87:17  الأية
وَالْآخِرَةُ خَيْرٌ وَأَبْقَىٰ
Wal-akhiratu khayrun waabqa

Hausa
 
Alhãli Lãhira ita ce mafi alheri kuma mafi wanzuwa.

Ayah  87:18  الأية
إِنَّ هَٰذَا لَفِي الصُّحُفِ الْأُولَىٰ
Inna hatha lafee assuhufial-oola

Hausa
 
Lalle ne, wannan yanã a cikin littafan farko.

Ayah  87:19  الأية
صُحُفِ إِبْرَاهِيمَ وَمُوسَىٰ
Suhufi ibraheema wamoosa

Hausa
 
Littaffan Ibrãhĩm da Mũsã.




© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us