Muhawara Hausa
 



ARBA'UNA HADITH (16) HADISI NA SHA SHIDA
 
Al'Adun Musulmi Da Darajoji ARBA'UNA HADITH (16) HADISI NA SHA SHIDA

An karbo daga Abu hurairata R.A yace, wani mutum yazo, yace da Annabi kayi min wasiyya saihhi yace dashi kada kai fushi sai kayi fushi sai yayi ta maimaita bukatarsa, si (Annabi) yace, kada kai fushi Bukhari (6116) ya rawaito.

SHARHI; Dangane da lafizin ''Wasiyya'' day a zo a cikin jumlar, ''Ku yi min wasiyya.'' Abin daake nufi da 'wasiyya', shi ne wata kalma takaitacciya d azan dade ina amfani da ita a cikin rayuwata a duniya, wadda za ta dora ni a kan tafarki madaidaci. Da y ace ''ka yi min wasiyya.'' Tsammaninsa Annabi (S.A.W).

zai rubuta masa lattafi guda, amma sai y ace masa ''kada ka yi fushi'' sai yayi ta maimata bukatarsa ta dazu, ''...... yi min wasiyya.'' Annabi (S.A.W). ya tsaya bai ce komai ba, ya kyale shi. To da aka ce, ''Kada ka yi fushi!'' ai fushi ba ikonka ban e, zuwa yake yi, ba ka san ya zo ba, ka duba Annabin Allah aka ba shi attura, aka ce da shi ''..... Rike tada karfi'' amma day a zo ya sami kansa a cikin fushi, ya jefar da attaura gaba-daya. Yayin day a huce, sai ya dauke ta. To yaya za ka yi, ba za ka yi fushi ba? Ai ba zai yiwu ba a hana ka abin dab a ya yiwuwa. Don haka sai dai a ce , cewar ''Kada ka yi fushi!'' yana da ma'ana guda biyu: wadansu suke ce ma'anar da za mu iya bayarwa wajen, ''kada ka yi fushi!'' shi ne sifanta da hallaye nagari, kamar karamci, da afuwa da yawan hakuri, da yawan kyauta, kar ka zamanto marowaci.

To idan ka siffantu da wannan siffofi, su ne za su taimaka maka, su rika rage maka yawan fushi. In ba ka da su kuwa, dole ka yi fushi. Saboda Annabi (S.A.W). y ace ''Kada ka yi fushi!'' kamar yana nfin ka siffantu da dabi'u nagari, irin dabi'un da suke rage fushin.

Ma'ana ta biyu suka ce, abin da ake nufi da ''kada ka yi fushi!'' shi ne, kada ka yi aiki da fushi in ya zo maka, kar ka zartar da hukunci kana cikin fushi. Domin indan fushi ya yi yawa, kila ka zo ka cewa matarka, ka sake ta saki uku! Daga baya ka zo kana ta bin malamai kana fatwa. Don haka duk abin da fushi ya shawarce ka, ka yi, kar ka yi aiki da wannan abin, ka nisanc shi, ka zamto mai hakuri, mai juriya. {Don ganin Karin bayani duba: Jami'ul Ulum walHikam Na Ibnu Rajab 1/373-374}.

Wannan wasiyya ta Annabi (S.A.W). ta shafi dukan dangogin ayyuka na alheri, kamar yadda malamai suke ce, wannan yana cikin jawami'ul Kalim da aka ba wa Annabi (S.A.W). Wato jumla guda daya, amma za ta dauki ma'ana mai dinbin yawa, domin za ta shiga cikin kowanne bangare na rayuwa.

Domin fushi yana iya sa ka yi abu ba dan Allah ba, sai ya zamanto ba ka samu lada ba wajen Allah.

An rawaito daga Aliyyu bin Abi Dalib wata rana ya fito wajen yaki ya dauki takobinsa, ya fuskanci wani kafiri gadan-gadan zai immasa, sai wannan kafiri ya tafa masa yawu, sai Aliyyu bin Abi Dalib ya fasa kashe shi, ya ja baya, ya ba shi wuri. Sai abi nya ba wa wannan kafirinm mamaki, y ace, ''Abul- Hasan! Da ka biyo ni kamar za ka kasheni, ni,m ga shi kuma ka samu damar ka kashe ni, amma da na taho maka yawu, sai ka fasa, Ya ce ''IE! Lokacin da na taho a karon farko, na z one da niya zan yake ka, don kai kafiri n, don daukaka kalmar Allah, in gama da kai musulunci ya ci gaba, amma da ka tofa min yawu, sai na ji haushi, sai na ji tsoron kai in kashe ka, ka dauka don ka tofa min yawu ne, ba don kasancewarka kafiri ba. Don haka sai na fasa.'' To ka ga a nan wurin fusihn da Annabi (S.A.W). yake hanawa, shi ne fushi don don kanka, kar ka yi fushi don ba da kariya ga kanka, ko ba kariba ga 'yan uwanka ko 'yan gidanku, don an take mutuncinsu. Kar ka yi fushi don wannan! Shi ne ma''anar ''Kada ka yi fushi!'' Share Sign out Notify me Comment as:

Publish Preview 1 comment:

Alhassan December 20, 2011 at 12:39 PM Wane mutum ne yazo wurin manzon Allah (SAW) don niman wasiya?

 Posted By Aka Sanya A Sunday, February 26 @ 05:28:30 PST Da MediaHausaTeam



Comments 💬 التعليقات
 

For Your Membership Comments And Registered Debates Please, See Below Or Register Here :-: للحصول على تعليقات عضويتك و مناقشات الأعضاء انظر من فضلك أدناه أو سجّل هنا

Hanyoyin da ke da alaƙa

· Ƙari Game da Al'Adun Musulmi Da Darajoji
· Labarai By MediaHausaTeam


Mafi Karanta Labari Game da Al'Adun Musulmi Da Darajoji:
Sahabban Manzon Allah (SAW) Kamar Yadda Hadisai Suka Bayyana Su


Matsalar Magana

Matsakaicin Maki: 0
Kurioi: 0

Don Allah a Ɗauki Na Biyu Ka Zabi Wannan Labarin:

Madalla
Mai kyau sosai
Mai kyau
Na yau da kullum
Bad


Zabuka


 Mawallafin Aboki Mawallafin Aboki





Ya Danganta Kanun Labarai

Al'Adun Musulmi Da Darajoji



"ARBA'UNA HADITH (16) HADISI NA SHA SHIDA" | Shiga/ Ƙirƙiri Asusu | 0 Lafiyata


Malakacin Bayanan na Mai aikawa. Ba Mu Da Alhaki Don Abubuwan da Suke ciki. A halin yanzu, Muna gayyatar masu karatu su ba da rahoton duk wani abu na cin zarafi, rashin dacewa da / ko abun ciki na Islama



Babu Sharhi Ta da Aka Bada izini Don Marasa Suna, Da fatan za a Yi rijista
 

Muhawara Hausa
Asusu Gare Ku
Babban Shafi  | Labarun Hausa  | Muhawara Hausa  | Ƙungiyar Hausa  | Saƙonninku Na Sirri  | Samiya Goma  | Batutuwa  | Takardun Labari  | Cagiya  | Yakan Yi Bitar  | Bincike  | Mujallan  | Ma\'ajiyar Takardu  | Shafin Yanar Gizo  | Saukewa  | Shawarce Mu


Ẹsin Islam الدين الإسلامي Religion of Islam Addinin Musulunci Agama Islam Religión del Islam 伊斯兰教 Dini ya Kiislamu Религия Ислам Religião do Islã イスラム教 Esin Islam 이슬람의 종교 Portal African Muslim Website - Arabic English African Islamic Website For World News, Fatwas, Audios, Videos, Muslim News, Articles, Radio, Audio, Video, Quran, Hadith, TV Channels, Fatwas, Muslim News, Newspapers, Magazines Headlines, Forums, College, Schools, Universities, Mosques, Quranic, Sunnah, Fiqh, Prayers, Salat, Ramadan, Vidoes, Books, Fasting, PDFs On EsinIslam.Com And IslamAfrica.Com