Prev  

44. Surah Ad-Dukhân سورة الدّخان

  Next  



Ayah  44:1  الأية
    +/- -/+  
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ

Ayah  44:2  الأية
    +/- -/+  

Ayah  44:3  الأية
    +/- -/+  
إِنَّا أَنزَلْنَاهُ فِي لَيْلَةٍ مُّبَارَكَةٍ ۚ إِنَّا كُنَّا مُنذِرِينَ
Hausa
 
Lalle ne, Mũ, Muka saukar da shi a cikin wani dare mai albarka. Lalle Mũ' Mun kasance Mãsu yin gargaɗi.

Ayah  44:4  الأية
    +/- -/+  
فِيهَا يُفْرَقُ كُلُّ أَمْرٍ حَكِيمٍ
Hausa
 
A cikinsa (shi daren) ake rarrabe kõwane umurui bayyananne.

Ayah  44:5  الأية
    +/- -/+  
أَمْرًا مِّنْ عِندِنَا ۚ إِنَّا كُنَّا مُرْسِلِينَ
Hausa
 
Umurni na daga wurinMu. Lalle Mũ ne Muka kasanceMãsu aikãwã.

Ayah  44:6  الأية
    +/- -/+  
رَحْمَةً مِّن رَّبِّكَ ۚ إِنَّهُ هُوَ السَّمِيعُ الْعَلِيمُ
Hausa
 
Sabõda rahama daga Ubangijinka. Lalle Shĩ, Shi ne Mai ji, Mãsani.

Ayah  44:7  الأية
    +/- -/+  
رَبِّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا ۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ
Hausa
 
(Shĩ ne) Ubangijin sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu yaƙĩni (za ku gãne haka).

Ayah  44:8  الأية
    +/- -/+  
لَا إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ يُحْيِي وَيُمِيتُ ۖ رَبُّكُمْ وَرَبُّ آبَائِكُمُ الْأَوَّلِينَ
Hausa
 
Babu abin bautãwa fãce Shi. Yana rãyarwa Kuma Yana kashẽwa. (Shi ne) Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko.

Ayah  44:9  الأية
    +/- -/+  

Ayah  44:10  الأية
    +/- -/+  
فَارْتَقِبْ يَوْمَ تَأْتِي السَّمَاءُ بِدُخَانٍ مُّبِينٍ
Hausa
 
Sabõda haka, ka dakata rãnar da sama zã tã zo da hayãƙi bayyananne.

Ayah  44:11  الأية
    +/- -/+  
يَغْشَى النَّاسَ ۖ هَٰذَا عَذَابٌ أَلِيمٌ
Hausa
 
Yanã rufe mutãne. Wannan wata azãba ce mai raɗaɗi.

Ayah  44:12  الأية
    +/- -/+  
رَّبَّنَا اكْشِفْ عَنَّا الْعَذَابَ إِنَّا مُؤْمِنُونَ
Hausa
 
Ya Ubangijinmu! Ka kuranye mana azãba. Lalle Mũ, mãsu ĩmãni ne.

Ayah  44:13  الأية
    +/- -/+  
أَنَّىٰ لَهُمُ الذِّكْرَىٰ وَقَدْ جَاءَهُمْ رَسُولٌ مُّبِينٌ
Hausa
 
Inã tunãwa take a gare su, alhãli kuwa, haƙĩƙa, Manzo mai bayyanãwa Ya je musu (da gargaɗin saukar azãbar, ba su karɓa ba)?

Ayah  44:14  الأية
    +/- -/+  
ثُمَّ تَوَلَّوْا عَنْهُ وَقَالُوا مُعَلَّمٌ مَّجْنُونٌ
Hausa
 
Sa'an nan suka jũya baya daga gare shi, Kuma suka ce: "Wanda ake gayãwa ne, mahaukaci."

Ayah  44:15  الأية
    +/- -/+  
إِنَّا كَاشِفُو الْعَذَابِ قَلِيلًا ۚ إِنَّكُمْ عَائِدُونَ
Hausa
 
Lalle Mũ, Mãsu kuranyẽwar azãba ne, a ɗan lõkaci kaɗan, lalle kũ, mãsu kõmãwa ne (ga laifin).

Ayah  44:16  الأية
    +/- -/+  
يَوْمَ نَبْطِشُ الْبَطْشَةَ الْكُبْرَىٰ إِنَّا مُنتَقِمُونَ
Hausa
 
Rãnar da Muke damƙa, damƙa mafi girma, lalle ne Mũ mãsu azãbar rãmuwa ne.

Ayah  44:17  الأية
    +/- -/+  
وَلَقَدْ فَتَنَّا قَبْلَهُمْ قَوْمَ فِرْعَوْنَ وَجَاءَهُمْ رَسُولٌ كَرِيمٌ
Hausa
 
Kuma lalle ne haƙĩƙa a gabaninsu, Mun fitini mutãnen Fir'auna, kuma wani Manzo karĩmi ya jẽ musu.

Ayah  44:18  الأية
    +/- -/+  
أَنْ أَدُّوا إِلَيَّ عِبَادَ اللهِ ۖ إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ
Hausa
 
(Mazon ya ce): "Ku kãwo mini (ĩmãninku) ya bayin Allah! Lalle ni, Manzo ne amintacce zuwa gare ku."

Ayah  44:19  الأية
    +/- -/+  
وَأَن لَّا تَعْلُوا عَلَى اللهِ ۖ إِنِّي آتِيكُم بِسُلْطَانٍ مُّبِينٍ
Hausa
 
"Kuma kada ku nẽmi ɗaukaka a kan Allah. Lalle nĩ mai zo muku ne da dalĩli bayyananne."

Ayah  44:20  الأية
    +/- -/+  
وَإِنِّي عُذْتُ بِرَبِّي وَرَبِّكُمْ أَن تَرْجُمُونِ
Hausa
 
"Kuma lalle nĩ na nẽmi tsari da Ubangijĩna, kuma Ubangijinku, dõmin kada ku jẽfe ni."

Ayah  44:21  الأية
    +/- -/+  
وَإِن لَّمْ تُؤْمِنُوا لِي فَاعْتَزِلُونِ
Hausa
 
"Kuma idan ba ku yi ĩmãni sabõda nĩ ba, to, ku nĩsance ni."

Ayah  44:22  الأية
    +/- -/+  
فَدَعَا رَبَّهُ أَنَّ هَٰؤُلَاءِ قَوْمٌ مُّجْرِمُونَ
Hausa
 
Sai ya kirayi Ubangjinsa cẽwa waɗannan mutãnene mãsu laifi.

Ayah  44:23  الأية
    +/- -/+  
فَأَسْرِ بِعِبَادِي لَيْلًا إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ
Hausa
 
(Allah Ya ce): "To, ka yi tafiyar dare da bayiNa, da dare. Lalle kũ, waɗanda ake bĩ ne (dõmin a kãma ku.)"

Ayah  44:24  الأية
    +/- -/+  
وَاتْرُكِ الْبَحْرَ رَهْوًا ۖ إِنَّهُمْ جُندٌ مُّغْرَقُونَ
Hausa
 
"Kuma ka bar tẽku rarrabe. Lalle sũ, runduna ce abar nutsarwa."

Ayah  44:25  الأية
    +/- -/+  
كَمْ تَرَكُوا مِن جَنَّاتٍ وَعُيُونٍ
Hausa
 
Da yawa suka bar gõnaki da marẽmari.

Ayah  44:26  الأية
    +/- -/+  

Ayah  44:27  الأية
    +/- -/+  
وَنَعْمَةٍ كَانُوا فِيهَا فَاكِهِينَ
Hausa
 
Da wata ni'ima da suka kasance a cikinta sunã mãsu hutu.

Ayah  44:28  الأية
    +/- -/+  
كَذَٰلِكَ ۖ وَأَوْرَثْنَاهَا قَوْمًا آخَرِينَ
Hausa
 
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da ita ga waɗansu mutãne na dabam.

Ayah  44:29  الأية
    +/- -/+  
فَمَا بَكَتْ عَلَيْهِمُ السَّمَاءُ وَالْأَرْضُ وَمَا كَانُوا مُنظَرِينَ
Hausa
 
Sa'an nan samã da ƙasã ba su yi kũka a kansu ba, Kuma ba su kasance waɗanda ake yi wa jinkiri ba.

Ayah  44:30  الأية
    +/- -/+  
وَلَقَدْ نَجَّيْنَا بَنِي إِسْرَائِيلَ مِنَ الْعَذَابِ الْمُهِينِ
Hausa
 
Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun tsĩrar da Banĩ Isrã'ĩla daga, azãba mai wulãkantãwa.

Ayah  44:31  الأية
    +/- -/+  
مِن فِرْعَوْنَ ۚ إِنَّهُ كَانَ عَالِيًا مِّنَ الْمُسْرِفِينَ
Hausa
 
Daga Fir'auna. Lalle shi, ya kasance maɗaukaki daga cikin mãsu ɓarna.

Ayah  44:32  الأية
    +/- -/+  
وَلَقَدِ اخْتَرْنَاهُمْ عَلَىٰ عِلْمٍ عَلَى الْعَالَمِينَ
Hausa
 
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe su sabõda wani ilmi (na Taurata) a kan mutãne.

Ayah  44:33  الأية
    +/- -/+  
وَآتَيْنَاهُم مِّنَ الْآيَاتِ مَا فِيهِ بَلَاءٌ مُّبِينٌ
Hausa
 
Kuma Muka bã su, daga ãyõyin mu'ujizõji, abin da yake a cikinsa, akwai ni'ima bayyananna

Ayah  44:34  الأية
    +/- -/+  

Ayah  44:35  الأية
    +/- -/+  
إِنْ هِيَ إِلَّا مَوْتَتُنَا الْأُولَىٰ وَمَا نَحْنُ بِمُنشَرِينَ
Hausa
 
"Babu wani abu sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake tãyarwa ba."

Ayah  44:36  الأية
    +/- -/+  
فَأْتُوا بِآبَائِنَا إِن كُنتُمْ صَادِقِينَ
Hausa
 
"Sai ku zo da ubanninmu, idan kun kasance mãsu gaskiya."

Ayah  44:37  الأية
    +/- -/+  
أَهُمْ خَيْرٌ أَمْ قَوْمُ تُبَّعٍ وَالَّذِينَ مِن قَبْلِهِمْ ۚ أَهْلَكْنَاهُمْ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا مُجْرِمِينَ
Hausa
 
shin, sũ ne mafĩfĩta kõ kuwa mutãnen Tubba'u, kuma da waɗanda ke a gabãninsu? Mun halaka su, lalle sũ, sun kasance mãsu laifi.

Ayah  44:38  الأية
    +/- -/+  
وَمَا خَلَقْنَا السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضَ وَمَا بَيْنَهُمَا لَاعِبِينَ
Hausa
 
Kuma ba Mu halitta slmmai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu ba, alhãli kuwa Munã mãsu wãsã.

Ayah  44:39  الأية
    +/- -/+  
مَا خَلَقْنَاهُمَا إِلَّا بِالْحَقِّ وَلَٰكِنَّ أَكْثَرَهُمْ لَا يَعْلَمُونَ
Hausa
 
Ba Mu halitta su ba fãce da manufa ta gaskiya, kuma amma mafi yawansu, ba su sani ba.

Ayah  44:40  الأية
    +/- -/+  
إِنَّ يَوْمَ الْفَصْلِ مِيقَاتُهُمْ أَجْمَعِينَ
Hausa
 
Lalle rãnar rarrabẽwa, ita ce lõkacin wa'adinsu gabã ɗaya.

Ayah  44:41  الأية
    +/- -/+  
يَوْمَ لَا يُغْنِي مَوْلًى عَن مَّوْلًى شَيْئًا وَلَا هُمْ يُنصَرُونَ
Hausa
 
Rãnar da wani zumu bã ya amfãnin wani zumu da kõme kuma ba su zama anã taimakon su ba.

Ayah  44:42  الأية
    +/- -/+  
إِلَّا مَن رَّحِمَ اللهُ ۚ إِنَّهُ هُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Hausa
 
fãce wanda Allah Ya yi wa rahama. Lalle Shi (Allah), shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Ayah  44:43  الأية
    +/- -/+  

Ayah  44:44  الأية
    +/- -/+  

Ayah  44:45  الأية
    +/- -/+  
كَالْمُهْلِ يَغْلِي فِي الْبُطُونِ
Hausa
 
Kamar narkakken kwalta yanã tafasa a cikin cikunna.

Ayah  44:46  الأية
    +/- -/+  

Ayah  44:47  الأية
    +/- -/+  
خُذُوهُ فَاعْتِلُوهُ إِلَىٰ سَوَاءِ الْجَحِيمِ
Hausa
 
(A cẽ wa malã'ikun wutã), "Ku kãmã shi, sa'an nan ku fizge shi zuwa ga tsakiyar Jahĩm."

Ayah  44:48  الأية
    +/- -/+  
ثُمَّ صُبُّوا فَوْقَ رَأْسِهِ مِنْ عَذَابِ الْحَمِيمِ
Hausa
 
"Sa'an nan ku zuba, a kansa, daga azãbar ruwan zãfi."

Ayah  44:49  الأية
    +/- -/+  
ذُقْ إِنَّكَ أَنتَ الْعَزِيزُ الْكَرِيمُ
Hausa
 
(A ce masã), "Ka ɗanɗana! Lalle kai, kai ne mabuwãyi mai girma!"

Ayah  44:50  الأية
    +/- -/+  
إِنَّ هَٰذَا مَا كُنتُم بِهِ تَمْتَرُونَ
Hausa
 
"Lalle wannan, shi ne abin da kuka kasance kunã shakka game da shi."

Ayah  44:51  الأية
    +/- -/+  
إِنَّ الْمُتَّقِينَ فِي مَقَامٍ أَمِينٍ
Hausa
 
Lalle mãsu taƙawa sunã cikin matsayi amintacce.

Ayah  44:52  الأية
    +/- -/+  

Ayah  44:53  الأية
    +/- -/+  
يَلْبَسُونَ مِن سُندُسٍ وَإِسْتَبْرَقٍ مُّتَقَابِلِينَ
Hausa
 
Sunã tufanta daga tufãfin alharĩni raƙĩƙi, da mai kauri, sunã mãsu zaman fuskantar jũna.

Ayah  44:54  الأية
    +/- -/+  
كَذَٰلِكَ وَزَوَّجْنَاهُم بِحُورٍ عِينٍ
Hausa
 
Kamar haka, kuma Mun aurar da su da mãtã mãsu kyaun idãnu, mãsu girmansu.

Ayah  44:55  الأية
    +/- -/+  
يَدْعُونَ فِيهَا بِكُلِّ فَاكِهَةٍ آمِنِينَ
Hausa
 
Sunã kira, a cikinsu (gidẽjen) ga dukan 'ya'yan itãcen marmari, sunã amintattu (daga dukan abin tsõro).

Ayah  44:56  الأية
    +/- -/+  
لَا يَذُوقُونَ فِيهَا الْمَوْتَ إِلَّا الْمَوْتَةَ الْأُولَىٰ ۖ وَوَقَاهُمْ عَذَابَ الْجَحِيمِ
Hausa
 
Bã su ɗanɗanar mutuwa, a cikinsu, fãce mutuwar farko, kuma (Allah), Ya tsare musu azãbar Jahĩm.

Ayah  44:57  الأية
    +/- -/+  
فَضْلًا مِّن رَّبِّكَ ۚ ذَٰلِكَ هُوَ الْفَوْزُ الْعَظِيمُ
Hausa
 
Sabõda falala daga Ubangijinka. Wancan shi ne babban rabo, mai girma.

Ayah  44:58  الأية
    +/- -/+  
فَإِنَّمَا يَسَّرْنَاهُ بِلِسَانِكَ لَعَلَّهُمْ يَتَذَكَّرُونَ
Hausa
 
Dõmin haka kawai Muka sauƙaƙar da shi (Alƙur'ãni) da harshenka, tsammãninsu, su riƙa tunãwa.

Ayah  44:59  الأية
    +/- -/+  
فَارْتَقِبْ إِنَّهُم مُّرْتَقِبُونَ
Hausa
 
Sai ka yi jira. Lalle sũ, mãsu jira ne.
 


© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us