« Prev

51. Surah Az-Zâriyât سورة الذاريات

Next »



First Ayah   1   الأية الأولي
بِسْم ِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ
وَالذَّارِيَاتِ ذَرْوًا
Hausa
 
Ină rantsuwa da iskőki măsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.

Ayah   51:2   الأية
فَالْحَامِلَاتِ وِقْرًا
Hausa
 
Sa'an nan da girăgizai măsu ɗaukar nauyi (na ruwa).

Ayah   51:3   الأية
فَالْجَارِيَاتِ يُسْرًا
Hausa
 
Sa'an nan da jirăge măsu gudăna (a kan ruwa) da sauƙi.

Ayah   51:4   الأية
فَالْمُقَسِّمَاتِ أَمْرًا
Hausa
 
Sa'an nan da Mală'iku măsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).

Ayah   51:5   الأية
إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَصَادِقٌ
Hausa
 
Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.

Ayah   51:6   الأية
وَإِنَّ الدِّينَ لَوَاقِعٌ
Hausa
 
Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne

Ayah   51:7   الأية
وَالسَّمَاءِ ذَاتِ الْحُبُكِ
Hausa
 
Ină rantsuwa da samă ma'abũciyar hanyőyi ( na tafiyar taurări da sautin rediyo).

Ayah   51:8   الأية
إِنَّكُمْ لَفِي قَوْلٍ مُّخْتَلِفٍ
Hausa
 
Lalle kũ, haƙĩƙa, kună cikin magana mai săɓa wa juna (game da Alƙur'ani).

Ayah   51:9   الأية
يُؤْفَكُ عَنْهُ مَنْ أُفِكَ
Hausa
 
Ană karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).

Ayah   51:10   الأية
قُتِلَ الْخَرَّاصُونَ
Hausa
 
An la'ani măsu ƙiri-faɗi.

Ayah   51:11   الأية
الَّذِينَ هُمْ فِي غَمْرَةٍ سَاهُونَ
Hausa
 
Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jăhilci.

Ayah   51:12   الأية
يَسْأَلُونَ أَيَّانَ يَوْمُ الدِّينِ
Hausa
 
Sună tambaya: "Yaushe ne rănar sakamako ză ta auku?"

Ayah   51:13   الأية
يَوْمَ هُمْ عَلَى النَّارِ يُفْتَنُونَ
Hausa
 
Ranar da suke a kan wuta ană fitinar su.

Ayah   51:14   الأية
ذُوقُوا فِتْنَتَكُمْ هَٰذَا الَّذِي كُنتُم بِهِ تَسْتَعْجِلُونَ
Hausa
 
(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kună nẽman zuwansa da gaggăwa."

Ayah   51:15   الأية
إِنَّ الْمُتَّقِينَ فِي جَنَّاتٍ وَعُيُونٍ
Hausa
 
Lalle măsu taƙawa, sună a cikin lambunan ităce da marẽmari.

Ayah   51:16   الأية
آخِذِينَ مَا آتَاهُمْ رَبُّهُمْ ۚ إِنَّهُمْ كَانُوا قَبْلَ ذَٰلِكَ مُحْسِنِينَ
Hausa
 
Sună măsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bă su. Lalle sũ, sun kasance măsu kyautatăwa a gabănin haka (a dũniya).

Ayah   51:17   الأية
كَانُوا قَلِيلًا مِّنَ اللَّيْلِ مَا يَهْجَعُونَ
Hausa
 
Sun kasance a lőkaci kaɗan na dare suke yin barci.

Ayah   51:18   الأية
وَبِالْأَسْحَارِ هُمْ يَسْتَغْفِرُونَ
Hausa
 
Kuma a lőkutan asuba sună ta yin istigfări.

Ayah   51:19   الأية
وَفِي أَمْوَالِهِمْ حَقٌّ لِّلسَّائِلِ وَالْمَحْرُومِ
Hausa
 
Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rőƙo da wanda aka hana wa rőƙo.

Ayah   51:20   الأية
وَفِي الْأَرْضِ آيَاتٌ لِّلْمُوقِنِينَ
Hausa
 
Kuma a cikin ƙasă akwai ăyőyi ga măsu yaƙĩni.

Ayah   51:21   الأية
وَفِي أَنفُسِكُمْ ۚ أَفَلَا تُبْصِرُونَ
Hausa
 
Kuma a cikin răyukanku (akwai ăyőyi). To, bă ză ku dũbă ba?

Ayah   51:22   الأية
وَفِي السَّمَاءِ رِزْقُكُمْ وَمَا تُوعَدُونَ
Hausa
 
Kuma a cikin sama arzikinku ( yake fitőwa) da abin da ake yi muku alkawari.

Ayah   51:23   الأية
فَوَرَبِّ السَّمَاءِ وَالْأَرْضِ إِنَّهُ لَحَقٌّ مِّثْلَ مَا أَنَّكُمْ تَنطِقُونَ
Hausa
 
To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasă, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kună karantăwa na magana,

Ayah   51:24   الأية
هَلْ أَتَاكَ حَدِيثُ ضَيْفِ إِبْرَاهِيمَ الْمُكْرَمِينَ
Hausa
 
Shin, lăbărin Băƙin Ibrăhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?

Ayah   51:25   الأية
إِذْ دَخَلُوا عَلَيْهِ فَقَالُوا سَلَامًا ۖ قَالَ سَلَامٌ قَوْمٌ مُّنكَرُونَ
Hausa
 
A lőkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutăne băƙi!"

Ayah   51:26   الأية
فَرَاغَ إِلَىٰ أَهْلِهِ فَجَاءَ بِعِجْلٍ سَمِينٍ
Hausa
 
Sai ya jũya zuwa ga iyălinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna,

Ayah   51:27   الأية
فَقَرَّبَهُ إِلَيْهِمْ قَالَ أَلَا تَأْكُلُونَ
Hausa
 
Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bă ză ku ci ba?"

Ayah   51:28   الأية
فَأَوْجَسَ مِنْهُمْ خِيفَةً ۖ قَالُوا لَا تَخَفْ ۖ وَبَشَّرُوهُ بِغُلَامٍ عَلِيمٍ
Hausa
 
Sai ya ji tsőro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsőro." Kuma suka yi masa bushăra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.

Ayah   51:29   الأية
فَأَقْبَلَتِ امْرَأَتُهُ فِي صَرَّةٍ فَصَكَّتْ وَجْهَهَا وَقَالَتْ عَجُوزٌ عَقِيمٌ
Hausa
 
Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallőwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsőhuwa bakarăriya (ză ta haihu)!"

Ayah   51:30   الأية
قَالُوا كَذَٰلِكِ قَالَ رَبُّكِ ۖ إِنَّهُ هُوَ الْحَكِيمُ الْعَلِيمُ
Hausa
 
Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."

Ayah   51:31   الأية
قَالَ فَمَا خَطْبُكُمْ أَيُّهَا الْمُرْسَلُونَ
Hausa
 
(Ibrăĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al'almarinku, yă kũ Manzanni!"

Ayah   51:32   الأية
قَالُوا إِنَّا أُرْسِلْنَا إِلَىٰ قَوْمٍ مُّجْرِمِينَ
Hausa
 
Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutăne, măsu laifi.

Ayah   51:33   الأية
لِنُرْسِلَ عَلَيْهِمْ حِجَارَةً مِّن طِينٍ
Hausa
 
"Dőmin mu saka musu waɗansu duwătsu na wani yumɓu ( bom).

Ayah   51:34   الأية
مُّسَوَّمَةً عِندَ رَبِّكَ لِلْمُسْرِفِينَ
Hausa
 
"Waɗanda aka yi wa alăma daga wajen Ubangijinka, dőmin măsu ɓarna."

Ayah   51:35   الأية
فَأَخْرَجْنَا مَن كَانَ فِيهَا مِنَ الْمُؤْمِنِينَ
Hausa
 
Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.

Ayah   51:36   الأية
فَمَا وَجَدْنَا فِيهَا غَيْرَ بَيْتٍ مِّنَ الْمُسْلِمِينَ
Hausa
 
Sai dai ba mu sămu ba, a cikinta, făce gida guda na Musulmi.

Ayah   51:37   الأية
وَتَرَكْنَا فِيهَا آيَةً لِّلَّذِينَ يَخَافُونَ الْعَذَابَ الْأَلِيمَ
Hausa
 
Kuma Muka bar wata ăyă, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsőron azăba, mai raɗaɗi.

Ayah   51:38   الأية
وَفِي مُوسَىٰ إِذْ أَرْسَلْنَاهُ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ بِسُلْطَانٍ مُّبِينٍ
Hausa
 
Kuma ga Mũsă, a lőkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalĩli bayyananne.

Ayah   51:39   الأية
فَتَوَلَّىٰ بِرُكْنِهِ وَقَالَ سَاحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌ
Hausa
 
Sai ya jũya băya tăre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kő kuwa mahaukaci !"

Ayah   51:40   الأية
فَأَخَذْنَاهُ وَجُنُودَهُ فَنَبَذْنَاهُمْ فِي الْيَمِّ وَهُوَ مُلِيمٌ
Hausa
 
Sabőda haka, Muka kama shi tăre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhăli kuwa yană wanda ake zargi.

Ayah   51:41   الأية
وَفِي عَادٍ إِذْ أَرْسَلْنَا عَلَيْهِمُ الرِّيحَ الْعَقِيمَ
Hausa
 
Kuma ga Ădăwa, a lőkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.

Ayah   51:42   الأية
مَا تَذَرُ مِن شَيْءٍ أَتَتْ عَلَيْهِ إِلَّا جَعَلَتْهُ كَالرَّمِيمِ
Hausa
 
Bă ta barin kőme da ta jẽ a kansa, făce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.

Ayah   51:43   الأية
وَفِي ثَمُودَ إِذْ قِيلَ لَهُمْ تَمَتَّعُوا حَتَّىٰ حِينٍ
Hausa
 
Kuma ga Samũdăwa, a lőkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dăɗi har wani ɗan lőkaci,"

Ayah   51:44   الأية
فَعَتَوْا عَنْ أَمْرِ رَبِّهِمْ فَأَخَذَتْهُمُ الصَّاعِقَةُ وَهُمْ يَنظُرُونَ
Hausa
 
Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabőda haka tsăwa ta kăma su, alhăli kuwa sună kallo.

Ayah   51:45   الأية
فَمَا اسْتَطَاعُوا مِن قِيَامٍ وَمَا كَانُوا مُنتَصِرِينَ
Hausa
 
Ba su kő sămu dămar tsayăwa ba, kuma ba su kasance măsu nẽman ăgaji ba.

Ayah   51:46   الأية
وَقَوْمَ نُوحٍ مِّن قَبْلُ ۖ إِنَّهُمْ كَانُوا قَوْمًا فَاسِقِينَ
Hausa
 
Da mutănen Nũhu a gabănin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutăne ne făsiƙai.

Ayah   51:47   الأية
وَالسَّمَاءَ بَنَيْنَاهَا بِأَيْدٍ وَإِنَّا لَمُوسِعُونَ
Hausa
 
Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhăli kuwa lalle Mũ ne Măsu yalwatăwa.

Ayah   51:48   الأية
وَالْأَرْضَ فَرَشْنَاهَا فَنِعْمَ الْمَاهِدُونَ
Hausa
 
Kuma ƙasă Mun shimfiɗa ta, To, madalla da măsu shimfiɗăwa, Mũ,

Ayah   51:49   الأية
وَمِن كُلِّ شَيْءٍ خَلَقْنَا زَوْجَيْنِ لَعَلَّكُمْ تَذَكَّرُونَ
Hausa
 
Kuma daga kőme Mun halitta nau'i biyu, watakila ză ku yi tunăni.

Ayah   51:50   الأية
فَفِرُّوا إِلَى اللَّهِ ۖ إِنِّي لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌ مُّبِينٌ
Hausa
 
Sabőda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.

Ayah   51:51   الأية
وَلَا تَجْعَلُوا مَعَ اللَّهِ إِلَٰهًا آخَرَ ۖ إِنِّي لَكُم مِّنْهُ نَذِيرٌ مُّبِينٌ
Hausa
 
Kuma kada ku sanya, tăre da Allah wani abin bautăwa na dabam, lalle nĩ, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.

Ayah   51:52   الأية
كَذَٰلِكَ مَا أَتَى الَّذِينَ مِن قَبْلِهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا قَالُوا سَاحِرٌ أَوْ مَجْنُونٌ
Hausa
 
Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabăninsu ba făce sun ce: "Mai sihiri ne kő mahaukaci."

Ayah   51:53   الأية
أَتَوَاصَوْا بِهِ ۚ بَلْ هُمْ قَوْمٌ طَاغُونَ
Hausa
 
shin, sună yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ă'a, sũ dai mutăne ne măsu girman kai.

Ayah   51:54   الأية
فَتَوَلَّ عَنْهُمْ فَمَا أَنتَ بِمَلُومٍ
Hausa
 
Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.

Ayah   51:55   الأية
وَذَكِّرْ فَإِنَّ الذِّكْرَىٰ تَنفَعُ الْمُؤْمِنِينَ
Hausa
 
Kuma ka tunătar, dőmin tunătarwa tană amfănin mũminai.

Ayah   51:56   الأية
وَمَا خَلَقْتُ الْجِنَّ وَالْإِنسَ إِلَّا لِيَعْبُدُونِ
Hausa
 
Kuma Ban halitta aljannu da mutăne ba sai dőmin su bauta Mini.

Ayah   51:57   الأية
مَا أُرِيدُ مِنْهُم مِّن رِّزْقٍ وَمَا أُرِيدُ أَن يُطْعِمُونِ
Hausa
 
Bă Ni nufln (sămun) wani arziki daga gare su, Bă Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.

Ayah   51:58   الأية
إِنَّ اللَّهَ هُوَ الرَّزَّاقُ ذُو الْقُوَّةِ الْمَتِينُ
Hausa
 
Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtăwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.

Ayah   51:59   الأية
فَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُوا ذَنُوبًا مِّثْلَ ذَنُوبِ أَصْحَابِهِمْ فَلَا يَسْتَعْجِلُونِ
Hausa
 
To, lalle waɗanda suka yi zălunci sună da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abőkansu, sabőda haka kada su yi Mini gaggăwa.

Ayah   51:60   الأية
فَوَيْلٌ لِّلَّذِينَ كَفَرُوا مِن يَوْمِهِمُ الَّذِي يُوعَدُونَ
Hausa
 
Sabőda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kăfirta, daga rănar su wadda aka yi musu alkawari.
 


© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us