Prev  

26. Surah Ash-Shu'arâ' سورة الشعراء

  Next  



Ayah  26:1  الأية
    +/- -/+  
بِسْم ِ اللهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيمِ

Ayah  26:2  الأية
    +/- -/+  
تِلْكَ آيَاتُ الْكِتَابِ الْمُبِينِ
Hausa
 
Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.

Ayah  26:3  الأية
    +/- -/+  
لَعَلَّكَ بَاخِعٌ نَّفْسَكَ أَلَّا يَكُونُوا مُؤْمِنِينَ
Hausa
 
Tsammãninka kai mai halakar da ranka ne, dõmin ba su kasance mũminai ba!

Ayah  26:4  الأية
    +/- -/+  
إِن نَّشَأْ نُنَزِّلْ عَلَيْهِم مِّنَ السَّمَاءِ آيَةً فَظَلَّتْ أَعْنَاقُهُمْ لَهَا خَاضِعِينَ
Hausa
 
Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.

Ayah  26:5  الأية
    +/- -/+  
وَمَا يَأْتِيهِم مِّن ذِكْرٍ مِّنَ الرَّحْمَٰنِ مُحْدَثٍ إِلَّا كَانُوا عَنْهُ مُعْرِضِينَ
Hausa
 
Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa.

Ayah  26:6  الأية
    +/- -/+  
فَقَدْ كَذَّبُوا فَسَيَأْتِيهِمْ أَنبَاءُ مَا كَانُوا بِهِ يَسْتَهْزِئُونَ
Hausa
 
To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.

Ayah  26:7  الأية
    +/- -/+  
أَوَلَمْ يَرَوْا إِلَى الْأَرْضِ كَمْ أَنبَتْنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوْجٍ كَرِيمٍ
Hausa
 
Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau?

Ayah  26:8  الأية
    +/- -/+  
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Hausa
 
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.

Ayah  26:9  الأية
    +/- -/+  
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Hausa
 
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.

Ayah  26:10  الأية
    +/- -/+  
وَإِذْ نَادَىٰ رَبُّكَ مُوسَىٰ أَنِ ائْتِ الْقَوْمَ الظَّالِمِينَ
Hausa
 
Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.

Ayah  26:11  الأية
    +/- -/+  
قَوْمَ فِرْعَوْنَ ۚ أَلَا يَتَّقُونَ
Hausa
 
"Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?"

Ayah  26:12  الأية
    +/- -/+  
قَالَ رَبِّ إِنِّي أَخَافُ أَن يُكَذِّبُونِ
Hausa
 
Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.

Ayah  26:13  الأية
    +/- -/+  
وَيَضِيقُ صَدْرِي وَلَا يَنطَلِقُ لِسَانِي فَأَرْسِلْ إِلَىٰ هَارُونَ
Hausa
 
"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.

Ayah  26:14  الأية
    +/- -/+  
وَلَهُمْ عَلَيَّ ذَنبٌ فَأَخَافُ أَن يَقْتُلُونِ
Hausa
 
"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."

Ayah  26:15  الأية
    +/- -/+  
قَالَ كَلَّا ۖ فَاذْهَبَا بِآيَاتِنَا ۖ إِنَّا مَعَكُم مُّسْتَمِعُونَ
Hausa
 
Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."

Ayah  26:16  الأية
    +/- -/+  
فَأْتِيَا فِرْعَوْنَ فَقُولَا إِنَّا رَسُولُ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
"Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."

Ayah  26:17  الأية
    +/- -/+  
أَنْ أَرْسِلْ مَعَنَا بَنِي إِسْرَائِيلَ
Hausa
 
"Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu."

Ayah  26:18  الأية
    +/- -/+  
قَالَ أَلَمْ نُرَبِّكَ فِينَا وَلِيدًا وَلَبِثْتَ فِينَا مِنْ عُمُرِكَ سِنِينَ
Hausa
 
Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"

Ayah  26:19  الأية
    +/- -/+  
وَفَعَلْتَ فَعْلَتَكَ الَّتِي فَعَلْتَ وَأَنتَ مِنَ الْكَافِرِينَ
Hausa
 
"Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?"

Ayah  26:20  الأية
    +/- -/+  
قَالَ فَعَلْتُهَا إِذًا وَأَنَا مِنَ الضَّالِّينَ
Hausa
 
Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin hushi."

Ayah  26:21  الأية
    +/- -/+  
فَفَرَرْتُ مِنكُمْ لَمَّا خِفْتُكُمْ فَوَهَبَ لِي رَبِّي حُكْمًا وَجَعَلَنِي مِنَ الْمُرْسَلِينَ
Hausa
 
"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."

Ayah  26:22  الأية
    +/- -/+  
وَتِلْكَ نِعْمَةٌ تَمُنُّهَا عَلَيَّ أَنْ عَبَّدتَّ بَنِي إِسْرَائِيلَ
Hausa
 
"Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla."

Ayah  26:23  الأية
    +/- -/+  
قَالَ فِرْعَوْنُ وَمَا رَبُّ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"

Ayah  26:24  الأية
    +/- -/+  
قَالَ رَبُّ السَّمَاوَاتِ وَالْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا ۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ
Hausa
 
Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."

Ayah  26:25  الأية
    +/- -/+  
قَالَ لِمَنْ حَوْلَهُ أَلَا تَسْتَمِعُونَ
Hausa
 
Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"

Ayah  26:26  الأية
    +/- -/+  
قَالَ رَبُّكُمْ وَرَبُّ آبَائِكُمُ الْأَوَّلِينَ
Hausa
 
Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."

Ayah  26:27  الأية
    +/- -/+  
قَالَ إِنَّ رَسُولَكُمُ الَّذِي أُرْسِلَ إِلَيْكُمْ لَمَجْنُونٌ
Hausa
 
Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."

Ayah  26:28  الأية
    +/- -/+  
قَالَ رَبُّ الْمَشْرِقِ وَالْمَغْرِبِ وَمَا بَيْنَهُمَا ۖ إِن كُنتُمْ تَعْقِلُونَ
Hausa
 
Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."

Ayah  26:29  الأية
    +/- -/+  
قَالَ لَئِنِ اتَّخَذْتَ إِلَٰهًا غَيْرِي لَأَجْعَلَنَّكَ مِنَ الْمَسْجُونِينَ
Hausa
 
Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."

Ayah  26:30  الأية
    +/- -/+  
قَالَ أَوَلَوْ جِئْتُكَ بِشَيْءٍ مُّبِينٍ
Hausa
 
Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"

Ayah  26:31  الأية
    +/- -/+  
قَالَ فَأْتِ بِهِ إِن كُنتَ مِنَ الصَّادِقِينَ
Hausa
 
Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya."

Ayah  26:32  الأية
    +/- -/+  
فَأَلْقَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ ثُعْبَانٌ مُّبِينٌ
Hausa
 
Sai ya jẽfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne.

Ayah  26:33  الأية
    +/- -/+  
وَنَزَعَ يَدَهُ فَإِذَا هِيَ بَيْضَاءُ لِلنَّاظِرِينَ
Hausa
 
Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo.

Ayah  26:34  الأية
    +/- -/+  
قَالَ لِلْمَلَإِ حَوْلَهُ إِنَّ هَٰذَا لَسَاحِرٌ عَلِيمٌ
Hausa
 
(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!

Ayah  26:35  الأية
    +/- -/+  
يُرِيدُ أَن يُخْرِجَكُم مِّنْ أَرْضِكُم بِسِحْرِهِ فَمَاذَا تَأْمُرُونَ
Hausa
 
"Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mẽne ne kuke shãwartãwa?"

Ayah  26:36  الأية
    +/- -/+  
قَالُوا أَرْجِهْ وَأَخَاهُ وَابْعَثْ فِي الْمَدَائِنِ حَاشِرِينَ
Hausa
 
Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."

Ayah  26:37  الأية
    +/- -/+  
يَأْتُوكَ بِكُلِّ سَحَّارٍ عَلِيمٍ
Hausa
 
"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."

Ayah  26:38  الأية
    +/- -/+  
فَجُمِعَ السَّحَرَةُ لِمِيقَاتِ يَوْمٍ مَّعْلُومٍ
Hausa
 
Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne.

Ayah  26:39  الأية
    +/- -/+  
وَقِيلَ لِلنَّاسِ هَلْ أَنتُم مُّجْتَمِعُونَ
Hausa
 
Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne?

Ayah  26:40  الأية
    +/- -/+  
لَعَلَّنَا نَتَّبِعُ السَّحَرَةَ إِن كَانُوا هُمُ الْغَالِبِينَ
Hausa
 
"Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya."

Ayah  26:41  الأية
    +/- -/+  
فَلَمَّا جَاءَ السَّحَرَةُ قَالُوا لِفِرْعَوْنَ أَئِنَّ لَنَا لَأَجْرًا إِن كُنَّا نَحْنُ الْغَالِبِينَ
Hausa
 
To, a lõkacin da masihirta suka jẽ suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?"

Ayah  26:42  الأية
    +/- -/+  
قَالَ نَعَمْ وَإِنَّكُمْ إِذًا لَّمِنَ الْمُقَرَّبِينَ
Hausa
 
Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai."

Ayah  26:43  الأية
    +/- -/+  
قَالَ لَهُم مُّوسَىٰ أَلْقُوا مَا أَنتُم مُّلْقُونَ
Hausa
 
Mũsã ya ce musu, "Ku jẽfa abin da kuke mãsu jẽfãwa."

Ayah  26:44  الأية
    +/- -/+  
فَأَلْقَوْا حِبَالَهُمْ وَعِصِيَّهُمْ وَقَالُوا بِعِزَّةِ فِرْعَوْنَ إِنَّا لَنَحْنُ الْغَالِبُونَ
Hausa
 
Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."

Ayah  26:45  الأية
    +/- -/+  
فَأَلْقَىٰ مُوسَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ تَلْقَفُ مَا يَأْفِكُونَ
Hausa
 
Sai Mũsa ya jẽfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya.

Ayah  26:46  الأية
    +/- -/+  
فَأُلْقِيَ السَّحَرَةُ سَاجِدِينَ
Hausa
 
Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.

Ayah  26:47  الأية
    +/- -/+  
قَالُوا آمَنَّا بِرَبِّ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."


Ayah  26:49  الأية
    +/- -/+  
قَالَ آمَنتُمْ لَهُ قَبْلَ أَنْ آذَنَ لَكُمْ ۖ إِنَّهُ لَكَبِيرُكُمُ الَّذِي عَلَّمَكُمُ السِّحْرَ فَلَسَوْفَ تَعْلَمُونَ ۚ لَأُقَطِّعَنَّ أَيْدِيَكُمْ وَأَرْجُلَكُم مِّنْ خِلَافٍ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمْ أَجْمَعِينَ
Hausa
 
Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa,zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya."

Ayah  26:50  الأية
    +/- -/+  
قَالُوا لَا ضَيْرَ ۖ إِنَّا إِلَىٰ رَبِّنَا مُنقَلِبُونَ
Hausa
 
Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."

Ayah  26:51  الأية
    +/- -/+  
إِنَّا نَطْمَعُ أَن يَغْفِرَ لَنَا رَبُّنَا خَطَايَانَا أَن كُنَّا أَوَّلَ الْمُؤْمِنِينَ
Hausa
 
"Lalle ne mu munã kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gãfarta mana kurakuranmu dõmin mun kasance farkon mãsu ĩmãni."

Ayah  26:52  الأية
    +/- -/+  
وَأَوْحَيْنَا إِلَىٰ مُوسَىٰ أَنْ أَسْرِ بِعِبَادِي إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ
Hausa
 
Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cẽwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã ne.

Ayah  26:53  الأية
    +/- -/+  
فَأَرْسَلَ فِرْعَوْنُ فِي الْمَدَائِنِ حَاشِرِينَ
Hausa
 
Sai Fir'auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne.

Ayah  26:54  الأية
    +/- -/+  
إِنَّ هَٰؤُلَاءِ لَشِرْذِمَةٌ قَلِيلُونَ
Hausa
 
"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."

Ayah  26:55  الأية
    +/- -/+  
وَإِنَّهُمْ لَنَا لَغَائِظُونَ
Hausa
 
"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."

Ayah  26:56  الأية
    +/- -/+  
وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَاذِرُونَ
Hausa
 
"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."

Ayah  26:57  الأية
    +/- -/+  
فَأَخْرَجْنَاهُم مِّن جَنَّاتٍ وَعُيُونٍ
Hausa
 
Sai Muka fitar da su daga gonaki da marẽmari.


Ayah  26:59  الأية
    +/- -/+  
كَذَٰلِكَ وَأَوْرَثْنَاهَا بَنِي إِسْرَائِيلَ
Hausa
 
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla.

Ayah  26:60  الأية
    +/- -/+  
فَأَتْبَعُوهُم مُّشْرِقِينَ
Hausa
 
Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.

Ayah  26:61  الأية
    +/- -/+  
فَلَمَّا تَرَاءَى الْجَمْعَانِ قَالَ أَصْحَابُ مُوسَىٰ إِنَّا لَمُدْرَكُونَ
Hausa
 
Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."

Ayah  26:62  الأية
    +/- -/+  
قَالَ كَلَّا ۖ إِنَّ مَعِيَ رَبِّي سَيَهْدِينِ
Hausa
 
Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."

Ayah  26:63  الأية
    +/- -/+  
فَأَوْحَيْنَا إِلَىٰ مُوسَىٰ أَنِ اضْرِب بِّعَصَاكَ الْبَحْرَ ۖ فَانفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرْقٍ كَالطَّوْدِ الْعَظِيمِ
Hausa
 
Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge, kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.

Ayah  26:64  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:65  الأية
    +/- -/+  
وَأَنجَيْنَا مُوسَىٰ وَمَن مَّعَهُ أَجْمَعِينَ
Hausa
 
Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.

Ayah  26:66  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:67  الأية
    +/- -/+  
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Hausa
 
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

Ayah  26:68  الأية
    +/- -/+  
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Hausa
 
Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.

Ayah  26:69  الأية
    +/- -/+  
وَاتْلُ عَلَيْهِمْ نَبَأَ إِبْرَاهِيمَ
Hausa
 
Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm.

Ayah  26:70  الأية
    +/- -/+  
إِذْ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوْمِهِ مَا تَعْبُدُونَ
Hausa
 
A sã'ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bauta wa?"

Ayah  26:71  الأية
    +/- -/+  
قَالُوا نَعْبُدُ أَصْنَامًا فَنَظَلُّ لَهَا عَاكِفِينَ
Hausa
 
Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."

Ayah  26:72  الأية
    +/- -/+  
قَالَ هَلْ يَسْمَعُونَكُمْ إِذْ تَدْعُونَ
Hausa
 
Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?"

Ayah  26:73  الأية
    +/- -/+  
أَوْ يَنفَعُونَكُمْ أَوْ يَضُرُّونَ
Hausa
 
"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"

Ayah  26:74  الأية
    +/- -/+  
قَالُوا بَلْ وَجَدْنَا آبَاءَنَا كَذَٰلِكَ يَفْعَلُونَ
Hausa
 
Suka ce: "Ã'a mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa."

Ayah  26:75  الأية
    +/- -/+  
قَالَ أَفَرَأَيْتُم مَّا كُنتُمْ تَعْبُدُونَ
Hausa
 
Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"

Ayah  26:76  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:77  الأية
    +/- -/+  
فَإِنَّهُمْ عَدُوٌّ لِّي إِلَّا رَبَّ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
"To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu."

Ayah  26:78  الأية
    +/- -/+  
الَّذِي خَلَقَنِي فَهُوَ يَهْدِينِ
Hausa
 
"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."

Ayah  26:79  الأية
    +/- -/+  
وَالَّذِي هُوَ يُطْعِمُنِي وَيَسْقِينِ
Hausa
 
"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."

Ayah  26:80  الأية
    +/- -/+  
وَإِذَا مَرِضْتُ فَهُوَ يَشْفِينِ
Hausa
 
"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."

Ayah  26:81  الأية
    +/- -/+  
وَالَّذِي يُمِيتُنِي ثُمَّ يُحْيِينِ
Hausa
 
"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."

Ayah  26:82  الأية
    +/- -/+  
وَالَّذِي أَطْمَعُ أَن يَغْفِرَ لِي خَطِيئَتِي يَوْمَ الدِّينِ
Hausa
 
"Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako."

Ayah  26:83  الأية
    +/- -/+  
رَبِّ هَبْ لِي حُكْمًا وَأَلْحِقْنِي بِالصَّالِحِينَ
Hausa
 
"Ya Ubangijĩna! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai."

Ayah  26:84  الأية
    +/- -/+  
وَاجْعَل لِّي لِسَانَ صِدْقٍ فِي الْآخِرِينَ
Hausa
 
"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya a cikin mutãnen ƙarshe."

Ayah  26:85  الأية
    +/- -/+  
وَاجْعَلْنِي مِن وَرَثَةِ جَنَّةِ النَّعِيمِ
Hausa
 
"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima."

Ayah  26:86  الأية
    +/- -/+  
وَاغْفِرْ لِأَبِي إِنَّهُ كَانَ مِنَ الضَّالِّينَ
Hausa
 
"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."

Ayah  26:87  الأية
    +/- -/+  
وَلَا تُخْزِنِي يَوْمَ يُبْعَثُونَ
Hausa
 
"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."

Ayah  26:88  الأية
    +/- -/+  
يَوْمَ لَا يَنفَعُ مَالٌ وَلَا بَنُونَ
Hausa
 
"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."

Ayah  26:89  الأية
    +/- -/+  
إِلَّا مَنْ أَتَى اللهَ بِقَلْبٍ سَلِيمٍ
Hausa
 
"Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki."

Ayah  26:90  الأية
    +/- -/+  
وَأُزْلِفَتِ الْجَنَّةُ لِلْمُتَّقِينَ
Hausa
 
Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.

Ayah  26:91  الأية
    +/- -/+  
وَبُرِّزَتِ الْجَحِيمُ لِلْغَاوِينَ
Hausa
 
Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.

Ayah  26:92  الأية
    +/- -/+  
وَقِيلَ لَهُمْ أَيْنَ مَا كُنتُمْ تَعْبُدُونَ
Hausa
 
Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"

Ayah  26:93  الأية
    +/- -/+  
مِن دُونِ اللهِ هَلْ يَنصُرُونَكُمْ أَوْ يَنتَصِرُونَ
Hausa
 
"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"

Ayah  26:94  الأية
    +/- -/+  
فَكُبْكِبُوا فِيهَا هُمْ وَالْغَاوُونَ
Hausa
 
Sai aka kikkife su a cikinta, su da halakakkun.

Ayah  26:95  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:96  الأية
    +/- -/+  
قَالُوا وَهُمْ فِيهَا يَخْتَصِمُونَ
Hausa
 
Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,

Ayah  26:97  الأية
    +/- -/+  
تَاللهِ إِن كُنَّا لَفِي ضَلَالٍ مُّبِينٍ
Hausa
 
"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."

Ayah  26:98  الأية
    +/- -/+  
إِذْ نُسَوِّيكُم بِرَبِّ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.

Ayah  26:99  الأية
    +/- -/+  
وَمَا أَضَلَّنَا إِلَّا الْمُجْرِمُونَ
Hausa
 
"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."

Ayah  26:100  الأية
    +/- -/+  


Ayah  26:102  الأية
    +/- -/+  
فَلَوْ أَنَّ لَنَا كَرَّةً فَنَكُونَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ
Hausa
 
"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"

Ayah  26:103  الأية
    +/- -/+  
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Hausa
 
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.

Ayah  26:104  الأية
    +/- -/+  
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Hausa
 
Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Ayah  26:105  الأية
    +/- -/+  
كَذَّبَتْ قَوْمُ نُوحٍ الْمُرْسَلِينَ
Hausa
 
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.

Ayah  26:106  الأية
    +/- -/+  
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ نُوحٌ أَلَا تَتَّقُونَ
Hausa
 
A lõkacin da ɗan'uwansu, Nũhu, ya ce musu, "Shin, bã zã ku yi taƙawa ba?"

Ayah  26:107  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:108  الأية
    +/- -/+  
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Hausa
 
"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Ayah  26:109  الأية
    +/- -/+  
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

Ayah  26:110  الأية
    +/- -/+  
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Hausa
 
"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Ayah  26:111  الأية
    +/- -/+  
قَالُوا أَنُؤْمِنُ لَكَ وَاتَّبَعَكَ الْأَرْذَلُونَ
Hausa
 
Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"

Ayah  26:112  الأية
    +/- -/+  
قَالَ وَمَا عِلْمِي بِمَا كَانُوا يَعْمَلُونَ
Hausa
 
Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."

Ayah  26:113  الأية
    +/- -/+  
إِنْ حِسَابُهُمْ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّي ۖ لَوْ تَشْعُرُونَ
Hausa
 
"Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancẽwa."

Ayah  26:114  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:115  الأية
    +/- -/+  
إِنْ أَنَا إِلَّا نَذِيرٌ مُّبِينٌ
Hausa
 
"Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa."

Ayah  26:116  الأية
    +/- -/+  
قَالُوا لَئِن لَّمْ تَنتَهِ يَا نُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ الْمَرْجُومِينَ
Hausa
 
Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"

Ayah  26:117  الأية
    +/- -/+  
قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوْمِي كَذَّبُونِ
Hausa
 
Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."

Ayah  26:118  الأية
    +/- -/+  
فَافْتَحْ بَيْنِي وَبَيْنَهُمْ فَتْحًا وَنَجِّنِي وَمَن مَّعِيَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ
Hausa
 
"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."

Ayah  26:119  الأية
    +/- -/+  
فَأَنجَيْنَاهُ وَمَن مَّعَهُ فِي الْفُلْكِ الْمَشْحُونِ
Hausa
 
Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.

Ayah  26:120  الأية
    +/- -/+  
ثُمَّ أَغْرَقْنَا بَعْدُ الْبَاقِينَ
Hausa
 
Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.

Ayah  26:121  الأية
    +/- -/+  
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Hausa
 
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

Ayah  26:122  الأية
    +/- -/+  
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Hausa
 
Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.

Ayah  26:123  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:124  الأية
    +/- -/+  
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ هُودٌ أَلَا تَتَّقُونَ
Hausa
 
A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

Ayah  26:125  الأية
    +/- -/+  
إِنِّي لَكُمْ رَسُولٌ أَمِينٌ
Hausa
 
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."

Ayah  26:126  الأية
    +/- -/+  
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Hausa
 
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Ayah  26:127  الأية
    +/- -/+  
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
"Kuma bã ni tambayar wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba, fãce daga Ubangijin halittu."

Ayah  26:128  الأية
    +/- -/+  
أَتَبْنُونَ بِكُلِّ رِيعٍ آيَةً تَعْبَثُونَ
Hausa
 
"Shin, kunã yin ginin sitadiyo a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"

Ayah  26:129  الأية
    +/- -/+  
وَتَتَّخِذُونَ مَصَانِعَ لَعَلَّكُمْ تَخْلُدُونَ
Hausa
 
"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?"

Ayah  26:130  الأية
    +/- -/+  
وَإِذَا بَطَشْتُم بَطَشْتُمْ جَبَّارِينَ
Hausa
 
"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."

Ayah  26:131  الأية
    +/- -/+  
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Hausa
 
"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Ayah  26:132  الأية
    +/- -/+  
وَاتَّقُوا الَّذِي أَمَدَّكُم بِمَا تَعْلَمُونَ
Hausa
 
"Ku ji tsõron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani."

Ayah  26:133  الأية
    +/- -/+  
أَمَدَّكُم بِأَنْعَامٍ وَبَنِينَ
Hausa
 
"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."


Ayah  26:135  الأية
    +/- -/+  
إِنِّي أَخَافُ عَلَيْكُمْ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍ
Hausa
 
"Lalle ne nĩ, inã ji muku tsõron azãbar wani yini mai girma."

Ayah  26:136  الأية
    +/- -/+  
قَالُوا سَوَاءٌ عَلَيْنَا أَوَعَظْتَ أَمْ لَمْ تَكُن مِّنَ الْوَاعِظِينَ
Hausa
 
Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Kã yi wa'azi kõ ba ka kasance daga mãsu wa'azi ba."

Ayah  26:137  الأية
    +/- -/+  
إِنْ هَٰذَا إِلَّا خُلُقُ الْأَوَّلِينَ
Hausa
 
"Wannan abu bai zamõ ba fãce hãlãyen mutãnen farko."

Ayah  26:138  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:139  الأية
    +/- -/+  
فَكَذَّبُوهُ فَأَهْلَكْنَاهُمْ ۗ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Hausa
 
Sabõda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da sũ.Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

Ayah  26:140  الأية
    +/- -/+  
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Hausa
 
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Ayah  26:141  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:142  الأية
    +/- -/+  
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ صَالِحٌ أَلَا تَتَّقُونَ
Hausa
 
A lõkacin da ɗan'uwansu Sãlihu ya ce: "Shin, bã zã ku bi Allah da taƙawa ba?"

Ayah  26:143  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:144  الأية
    +/- -/+  
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Hausa
 
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.

Ayah  26:145  الأية
    +/- -/+  
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba fãce da a Ubangijin halittu."

Ayah  26:146  الأية
    +/- -/+  
أَتُتْرَكُونَ فِي مَا هَاهُنَا آمِنِينَ
Hausa
 
"Shin, anã barin ku a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"


Ayah  26:148  الأية
    +/- -/+  
وَزُرُوعٍ وَنَخْلٍ طَلْعُهَا هَضِيمٌ
Hausa
 
"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi mãsu narkẽwa a ciki?"

Ayah  26:149  الأية
    +/- -/+  
وَتَنْحِتُونَ مِنَ الْجِبَالِ بُيُوتًا فَارِهِينَ
Hausa
 
"Kuma kunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, kunã mãsu alfãhari?"

Ayah  26:150  الأية
    +/- -/+  
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Hausa
 
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Ayah  26:151  الأية
    +/- -/+  
وَلَا تُطِيعُوا أَمْرَ الْمُسْرِفِينَ
Hausa
 
"Kada ku yi ɗã'ã ga umurnin maɓarnata."

Ayah  26:152  الأية
    +/- -/+  
الَّذِينَ يُفْسِدُونَ فِي الْأَرْضِ وَلَا يُصْلِحُونَ
Hausa
 
"Waɗanda suke yin ɓarna a cikin ƙasa, kuma bã su kyautatãwa."

Ayah  26:153  الأية
    +/- -/+  
قَالُوا إِنَّمَا أَنتَ مِنَ الْمُسَحَّرِينَ
Hausa
 
Suka ce: "Kai daga mãsu sihiri kurum kake."

Ayah  26:154  الأية
    +/- -/+  
مَا أَنتَ إِلَّا بَشَرٌ مِّثْلُنَا فَأْتِ بِآيَةٍ إِن كُنتَ مِنَ الصَّادِقِينَ
Hausa
 
"Bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu. To, kã zo da wata ãyã idan kã kasance daga mãsu gaskiya."

Ayah  26:155  الأية
    +/- -/+  
قَالَ هَٰذِهِ نَاقَةٌ لَّهَا شِرْبٌ وَلَكُمْ شِرْبُ يَوْمٍ مَّعْلُومٍ
Hausa
 
Ya ce: "Wannan rãkuma ce tanã da shan yini, kuma kunã da shan yini sasanne."

Ayah  26:156  الأية
    +/- -/+  
وَلَا تَمَسُّوهَا بِسُوءٍ فَيَأْخُذَكُمْ عَذَابُ يَوْمٍ عَظِيمٍ
Hausa
 
"Kada ku shãfe ta da cũta har azãbar yini mai girmã ta shãfe ku."

Ayah  26:157  الأية
    +/- -/+  
فَعَقَرُوهَا فَأَصْبَحُوا نَادِمِينَ
Hausa
 
Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.

Ayah  26:158  الأية
    +/- -/+  
فَأَخَذَهُمُ الْعَذَابُ ۗ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Hausa
 
Sabõda haka azãba ta kãma su. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

Ayah  26:159  الأية
    +/- -/+  
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Hausa
 
Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.

Ayah  26:160  الأية
    +/- -/+  
كَذَّبَتْ قَوْمُ لُوطٍ الْمُرْسَلِينَ
Hausa
 
Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata Manzanni.

Ayah  26:161  الأية
    +/- -/+  
إِذْ قَالَ لَهُمْ أَخُوهُمْ لُوطٌ أَلَا تَتَّقُونَ
Hausa
 
A lõkacin da ɗan'uwansu, Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

Ayah  26:162  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:163  الأية
    +/- -/+  
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Hausa
 
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."

Ayah  26:164  الأية
    +/- -/+  
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra, Ijãrãta ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

Ayah  26:165  الأية
    +/- -/+  
أَتَأْتُونَ الذُّكْرَانَ مِنَ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
"Shin kunã jẽ wa maza daga cikin talikai?"

Ayah  26:166  الأية
    +/- -/+  
وَتَذَرُونَ مَا خَلَقَ لَكُمْ رَبُّكُم مِّنْ أَزْوَاجِكُم ۚ بَلْ أَنتُمْ قَوْمٌ عَادُونَ
Hausa
 
"Kuma kunã barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga mãtanku? Ã'a, ku mutãne ne mãsu ƙẽtarẽwa!"

Ayah  26:167  الأية
    +/- -/+  
قَالُوا لَئِن لَّمْ تَنتَهِ يَا لُوطُ لَتَكُونَنَّ مِنَ الْمُخْرَجِينَ
Hausa
 
Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."

Ayah  26:168  الأية
    +/- -/+  
قَالَ إِنِّي لِعَمَلِكُم مِّنَ الْقَالِينَ
Hausa
 
Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa."

Ayah  26:169  الأية
    +/- -/+  
رَبِّ نَجِّنِي وَأَهْلِي مِمَّا يَعْمَلُونَ
Hausa
 
"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."

Ayah  26:170  الأية
    +/- -/+  
فَنَجَّيْنَاهُ وَأَهْلَهُ أَجْمَعِينَ
Hausa
 
Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.

Ayah  26:171  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:172  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:173  الأية
    +/- -/+  
وَأَمْطَرْنَا عَلَيْهِم مَّطَرًا ۖ فَسَاءَ مَطَرُ الْمُنذَرِينَ
Hausa
 
Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana.

Ayah  26:174  الأية
    +/- -/+  
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Hausa
 
Lalle ne ga wannan, akwai ãyã, kuma mafi yawansu bã su kasance mãsu ĩmãni ba.

Ayah  26:175  الأية
    +/- -/+  
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Hausa
 
Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Ayah  26:176  الأية
    +/- -/+  
كَذَّبَ أَصْحَابُ الْأَيْكَةِ الْمُرْسَلِينَ
Hausa
 
Ma'abũta ƙunci sun ƙaryata Manzanni.

Ayah  26:177  الأية
    +/- -/+  
إِذْ قَالَ لَهُمْ شُعَيْبٌ أَلَا تَتَّقُونَ
Hausa
 
A lõkacin da Shu'aibu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"

Ayah  26:178  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:179  الأية
    +/- -/+  
فَاتَّقُوا اللهَ وَأَطِيعُونِ
Hausa
 
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."

Ayah  26:180  الأية
    +/- -/+  
وَمَا أَسْأَلُكُمْ عَلَيْهِ مِنْ أَجْرٍ ۖ إِنْ أَجْرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
"Kuma ba ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."

Ayah  26:181  الأية
    +/- -/+  
أَوْفُوا الْكَيْلَ وَلَا تَكُونُوا مِنَ الْمُخْسِرِينَ
Hausa
 
"Ku cika mũdu, kuma kada ku kasance daga mãsu sanyãwar hasãra (ga mutãne)."

Ayah  26:182  الأية
    +/- -/+  
وَزِنُوا بِالْقِسْطَاسِ الْمُسْتَقِيمِ
Hausa
 
"Kuma ku yi awo da sikẽli daidaitacce."

Ayah  26:183  الأية
    +/- -/+  
وَلَا تَبْخَسُوا النَّاسَ أَشْيَاءَهُمْ وَلَا تَعْثَوْا فِي الْأَرْضِ مُفْسِدِينَ
Hausa
 
"Kuma kada ku nakasa wa mutãne abũbuwansu kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa kuna mãsu ɓarna."

Ayah  26:184  الأية
    +/- -/+  
وَاتَّقُوا الَّذِي خَلَقَكُمْ وَالْجِبِلَّةَ الْأَوَّلِينَ
Hausa
 
"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."

Ayah  26:185  الأية
    +/- -/+  
قَالُوا إِنَّمَا أَنتَ مِنَ الْمُسَحَّرِينَ
Hausa
 
Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne."

Ayah  26:186  الأية
    +/- -/+  
وَمَا أَنتَ إِلَّا بَشَرٌ مِّثْلُنَا وَإِن نَّظُنُّكَ لَمِنَ الْكَاذِبِينَ
Hausa
 
"Kuma bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu kuma lalle ne munã zaton ka, haƙĩƙa, daga maƙaryata."

Ayah  26:187  الأية
    +/- -/+  
فَأَسْقِطْ عَلَيْنَا كِسَفًا مِّنَ السَّمَاءِ إِن كُنتَ مِنَ الصَّادِقِينَ
Hausa
 
"To ka jẽfo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga mãsu gaskiya."

Ayah  26:188  الأية
    +/- -/+  
قَالَ رَبِّي أَعْلَمُ بِمَا تَعْمَلُونَ
Hausa
 
Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa."

Ayah  26:189  الأية
    +/- -/+  
فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَهُمْ عَذَابُ يَوْمِ الظُّلَّةِ ۚ إِنَّهُ كَانَ عَذَابَ يَوْمٍ عَظِيمٍ
Hausa
 
Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma.

Ayah  26:190  الأية
    +/- -/+  
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَآيَةً ۖ وَمَا كَانَ أَكْثَرُهُم مُّؤْمِنِينَ
Hausa
 
Lalle a cikin wancan haƙĩka akwai ãya, amma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.

Ayah  26:191  الأية
    +/- -/+  
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ الْعَزِيزُ الرَّحِيمُ
Hausa
 
Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Ayah  26:192  الأية
    +/- -/+  
وَإِنَّهُ لَتَنزِيلُ رَبِّ الْعَالَمِينَ
Hausa
 
Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.

Ayah  26:193  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:194  الأية
    +/- -/+  
عَلَىٰ قَلْبِكَ لِتَكُونَ مِنَ الْمُنذِرِينَ
Hausa
 
A kan zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.

Ayah  26:195  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:196  الأية
    +/- -/+  
وَإِنَّهُ لَفِي زُبُرِ الْأَوَّلِينَ
Hausa
 
Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.

Ayah  26:197  الأية
    +/- -/+  
أَوَلَمْ يَكُن لَّهُمْ آيَةً أَن يَعْلَمَهُ عُلَمَاءُ بَنِي إِسْرَائِيلَ
Hausa
 
Ashe, bai kasance ãyã ba a gare su, ya zama Mãlaman Banĩ Isrã'ĩla sun san shi?

Ayah  26:198  الأية
    +/- -/+  
وَلَوْ نَزَّلْنَاهُ عَلَىٰ بَعْضِ الْأَعْجَمِينَ
Hausa
 
Kuma dã mun saukar da shi a kan sãshen Ajamãwa,

Ayah  26:199  الأية
    +/- -/+  
فَقَرَأَهُ عَلَيْهِم مَّا كَانُوا بِهِ مُؤْمِنِينَ
Hausa
 
Ya karanta shi a kansu, ba su kasance sabõda shi mãsu ĩmãni ba.

Ayah  26:200  الأية
    +/- -/+  
كَذَٰلِكَ سَلَكْنَاهُ فِي قُلُوبِ الْمُجْرِمِينَ
Hausa
 
Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.

Ayah  26:201  الأية
    +/- -/+  
لَا يُؤْمِنُونَ بِهِ حَتَّىٰ يَرَوُا الْعَذَابَ الْأَلِيمَ
Hausa
 
Bã zã su yi ĩmãni da shĩ ba sai sun ga azãbar nan mai raɗadi.

Ayah  26:202  الأية
    +/- -/+  
فَيَأْتِيَهُم بَغْتَةً وَهُمْ لَا يَشْعُرُونَ
Hausa
 
Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba.

Ayah  26:203  الأية
    +/- -/+  
فَيَقُولُوا هَلْ نَحْنُ مُنظَرُونَ
Hausa
 
Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?"

Ayah  26:204  الأية
    +/- -/+  
أَفَبِعَذَابِنَا يَسْتَعْجِلُونَ
Hausa
 
Ashe, to, da azãbarMu suke nẽman gaggãwa?

Ayah  26:205  الأية
    +/- -/+  
أَفَرَأَيْتَ إِن مَّتَّعْنَاهُمْ سِنِينَ
Hausa
 
Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,

Ayah  26:206  الأية
    +/- -/+  
ثُمَّ جَاءَهُم مَّا كَانُوا يُوعَدُونَ
Hausa
 
Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,

Ayah  26:207  الأية
    +/- -/+  
مَا أَغْنَىٰ عَنْهُم مَّا كَانُوا يُمَتَّعُونَ
Hausa
 
Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare su.

Ayah  26:208  الأية
    +/- -/+  
وَمَا أَهْلَكْنَا مِن قَرْيَةٍ إِلَّا لَهَا مُنذِرُونَ
Hausa
 
Kuma bã Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da mãsu gargaɗi.

Ayah  26:209  الأية
    +/- -/+  
ذِكْرَىٰ وَمَا كُنَّا ظَالِمِينَ
Hausa
 
Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba.

Ayah  26:210  الأية
    +/- -/+  
وَمَا تَنَزَّلَتْ بِهِ الشَّيَاطِينُ
Hausa
 
Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.

Ayah  26:211  الأية
    +/- -/+  
وَمَا يَنبَغِي لَهُمْ وَمَا يَسْتَطِيعُونَ
Hausa
 
Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.

Ayah  26:212  الأية
    +/- -/+  
إِنَّهُمْ عَنِ السَّمْعِ لَمَعْزُولُونَ
Hausa
 
Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.

Ayah  26:213  الأية
    +/- -/+  
فَلَا تَدْعُ مَعَ اللهِ إِلَٰهًا آخَرَ فَتَكُونَ مِنَ الْمُعَذَّبِينَ
Hausa
 
Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.

Ayah  26:214  الأية
    +/- -/+  
وَأَنذِرْ عَشِيرَتَكَ الْأَقْرَبِينَ
Hausa
 
Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.

Ayah  26:215  الأية
    +/- -/+  
وَاخْفِضْ جَنَاحَكَ لِمَنِ اتَّبَعَكَ مِنَ الْمُؤْمِنِينَ
Hausa
 
Kuma ka sassauta fikãfikanka ga wanda ya bĩ ka daga mũminai.

Ayah  26:216  الأية
    +/- -/+  
فَإِنْ عَصَوْكَ فَقُلْ إِنِّي بَرِيءٌ مِّمَّا تَعْمَلُونَ
Hausa
 
Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."

Ayah  26:217  الأية
    +/- -/+  
وَتَوَكَّلْ عَلَى الْعَزِيزِ الرَّحِيمِ
Hausa
 
Kuma ka dõgara ga Mabuwãyi, Mai jin ƙai.

Ayah  26:218  الأية
    +/- -/+  
الَّذِي يَرَاكَ حِينَ تَقُومُ
Hausa
 
Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye.

Ayah  26:219  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:220  الأية
    +/- -/+  

Ayah  26:221  الأية
    +/- -/+  
هَلْ أُنَبِّئُكُمْ عَلَىٰ مَن تَنَزَّلُ الشَّيَاطِينُ
Hausa
 
Shin, (kunã so) in gaya muku a kan wanda Shaiɗãnnu kan sauka?

Ayah  26:222  الأية
    +/- -/+  
تَنَزَّلُ عَلَىٰ كُلِّ أَفَّاكٍ أَثِيمٍ
Hausa
 
Sukan sauka a kan dukkan maƙaryaci, mai zunubi.

Ayah  26:223  الأية
    +/- -/+  
يُلْقُونَ السَّمْعَ وَأَكْثَرُهُمْ كَاذِبُونَ
Hausa
 
Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.

Ayah  26:224  الأية
    +/- -/+  
وَالشُّعَرَاءُ يَتَّبِعُهُمُ الْغَاوُونَ
Hausa
 
Kuma mawãƙa halakakku ne ke bin su.

Ayah  26:225  الأية
    +/- -/+  
أَلَمْ تَرَ أَنَّهُمْ فِي كُلِّ وَادٍ يَهِيمُونَ
Hausa
 
Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?

Ayah  26:226  الأية
    +/- -/+  
وَأَنَّهُمْ يَقُولُونَ مَا لَا يَفْعَلُونَ
Hausa
 
Kuma lalle ne, sũ, sunã faɗin abin da bã su aikatãwa?

Ayah  26:227  الأية
    +/- -/+  
إِلَّا الَّذِينَ آمَنُوا وَعَمِلُوا الصَّالِحَاتِ وَذَكَرُوا اللهَ كَثِيرًا وَانتَصَرُوا مِن بَعْدِ مَا ظُلِمُوا ۗ وَسَيَعْلَمُ الَّذِينَ ظَلَمُوا أَيَّ مُنقَلَبٍ يَنقَلِبُونَ
Hausa
 
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka ambaci Allah da yawa, kuma suka rãma zãlunci, daga bãyan an zãlunce su. Kuma waɗanda suka yi zãlunci, zã su sani a wace majũya suke jũyãwa. 
 


© EsinIslam.Com Designed & produced by The Awqaf London. Please pray for us